< Romawa 11 >

1 To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
Jeg siger da: Mon Gud har forskudt sit Folk? Det være langt fra! Thi ogsaa jeg er en Israelit, af Abrahams Sæd, Benjamins Stamme.
2 Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
Gud har ikke forskudt sit Folk, som han forud kendte. Eller vide I ikke, hvad Skriften siger i Stykket om Elias? hvorledes han træder frem for Gud imod Israel, sigende:
3 “Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
„Herre! dine Profeter have de ihjelslaaet, dine Altre have de nedbrudt, og jeg er den eneste, der er levnet, og de efterstræbe mit Liv.”
4 Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
Men hvad siger det guddommelige Gensvar til ham? „Jeg har levnet mig selv syv Tusinde Mænd, som ikke have bøjet Knæ for Baal.”
5 Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
Saaledes er der da ogsaa i den nærværende Tid blevet en Levning som et Naades-Udvalg.
6 In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
Men er det af Naade, da er det ikke mere af Gerninger, ellers bliver Naaden ikke mere Naade.
7 To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
Hvad altsaa? Det, Israel søger efter, har det ikke opnaaet, men Udvalget har opnaaet det; de øvrige derimod bleve forhærdede,
8 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
som der er skrevet: „Gud gav dem en Sløvheds Aand, Øjne til ikke at se med, Øren til ikke at høre med indtil den Dag i Dag.”
9 Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
Og David siger: „Deres Bord vorde til Snare og til Fælde og til Anstød og til Gengældelse for dem;
10 Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
deres Øjne vorde formørkede, saa de ikke se, og bøj altid deres Ryg!”
11 Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
Jeg siger da: Mon de have stødt an, for at de skulde falde? Det være langt fra! Men ved deres Fald er Frelsen kommen til Hedningerne, for at dette kunde vække dem til Nidkærhed.
12 Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
Men dersom deres Fald er Verdens Rigdom, og deres Tab er Hedningers Rigdom, hvor meget mere skal deres Fylde være det!
13 Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
Og til eder, I Hedninger, siger jeg: For saa vidt jeg nu er Hedningeapostel, ærer jeg min Tjeneste,
14 da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
om jeg dog kunde vække min Slægt til Nidkærhed og frelse nogle af dem.
15 Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
Thi dersom deres Forkastelse er Verdens Forligelse, hvad bliver da deres Antagelse andet end Liv ud af døde?
16 In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
Men dersom Førstegrøden er hellig, da er Dejgen det ogsaa; og dersom Roden er hellig, da ere Grenene det ogsaa.
17 In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
Men om nogle af Grenene bleve afbrudte, og du, en vild Oliekvist, blev indpodet iblandt dem og blev meddelagtig i Olietræets Rod og Fedme,
18 kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
da ros dig ikke imod Grenene; men dersom du roser dig, da bærer jo ikke du Roden, men Roden dig.
19 To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
Du vil vel sige: Grene bleve afbrudte, for at jeg skulde blive indpodet.
20 Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
Vel! ved deres Vantro bleve de afbrudte, men du staar ved din Tro; vær ikke overmodig, men frygt!
21 Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
Thi naar Gud ikke sparede de naturlige Grene, vil han heller ikke spare dig.
22 Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
Saa se da Guds Godhed og Strenghed: Over dem, som faldt, er der Strenghed, men over dig Guds Godhed, hvis du bliver i hans Godhed; ellers skal ogsaa du afhugges.
23 In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
Men ogsaa hine skulle indpodes, dersom de ikke blive i Vantroen; thi Gud er mægtig til atter at indpode dem.
24 Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
Thi naar du blev afhugget af det Olietræ, som er vildt af Naturen, og imod Naturen blev indpodet i et ædelt Olietræ, hvor meget mere skulle da disse indpodes i deres eget Olietræ, som de af Natur tilhøre!
25 Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
Thi jeg vil ikke, Brødre! at I skulle være uvidende om denne Hemmelighed, for at I ikke skulle være kloge i eders egne Tanker, at Forhærdelse delvis er kommen over Israel, indtil Hedningernes Fylde er gaaet ind;
26 Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
og saa skal hele Israel frelses, som der er skrevet: „Fra Zion skal Befrieren komme, han skal afvende Ugudeligheder fra Jakob;
27 Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
og dette er min Pagt med dem, naar jeg borttager deres Synder.”
28 Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
Efter Evangeliet ere de vel Fjender for eders Skyld, men efter Udvælgelsen ere de elskede for Fædrenes Skyld;
29 gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
thi Naadegaverne og sit Kald fortryder Gud ikke.
30 Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
Thi ligesom I tilforn bleve ulydige imod Gud, men nu fik Barmhjertighed ved disses Ulydighed,
31 haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
saaledes bleve ogsaa disse nu ulydige, for at ogsaa de maatte faa Barmhjertighed ved den Barmhjertighed, som er bleven eder til Del.
32 Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē g1653)
Thi Gud har indesluttet alle under Ulydighed, for at han kunde forbarme sig over alle. (eleēsē g1653)
33 Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
O Dyb af Guds Rigdom og Visdom og Kundskab! hvor uransagelige ere hans Domme, og hans Veje usporlige!
34 “Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
Thi hvem har kendt Herrens Sind? eller hvem blev hans Raadgiver?
35 “Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
eller hvem gav ham først, saa at der skulde gives ham Gengæld derfor?
36 Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn g165)
Thi af ham og ved ham og til ham ere alle Ting; ham være Ære i Evighed! Amen. (aiōn g165)

< Romawa 11 >