< Romawa 10 >
1 ’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
Brāļi, mana sirds vēlēšanās un Dieva lūgšana par Israēla bērniem ir, ka tie tiek pestīti.
2 Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
Jo es tiem liecību dodu, ka tie karsti dzenās pēc Dieva, bet bez saprašanas.
3 Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
Jo nepazīdami Dieva taisnību un meklēdami uzcelt savu pašu taisnību, tie Dieva taisnībai nav paklausījuši.
4 Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
Jo bauslības gals ir Kristus, par taisnību ikvienam, kas tic.
5 Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
Jo Mozus raksta par to taisnību, kas nāk no bauslības: kurš cilvēks to dara, tas caur to dzīvos.
6 Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
Bet tā taisnība, kas no ticības, saka tā: nesaki savā sirdī, kas uzkāps debesīs? Proti Kristu novest zemē.
7 “ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos )
Jeb: kas nokāps bezdibenī? Proti Kristu no miroņiem atvest. (Abyssos )
8 Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
Bet ko tā saka? Tuvu pie tevis ir tas vārds, tavā mutē un tavā sirdī: proti tas ticības vārds, ko mēs pasludinājām.
9 Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
Jo ja tu ar savu muti Jēzu apliecināsi par Kungu un savā sirdī ticēsi, ka Dievs Viņu no miroņiem ir uzmodinājis, tad tu mūžīgi dzīvosi.
10 Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
Jo ar sirdi tic uz taisnību un ar muti apliecina uz mūžīgu dzīvošanu.
11 Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
Jo tas raksts saka: neviens, kas uz Viņu tic, nepaliks kaunā.
12 Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
Jo še nav starpības starp Jūdiem un Grieķiem, jo Tas pats ir Kungs pār visiem, bagāts priekš visiem, kas Viņu piesauc.
13 gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
Jo ikviens, kas Tā Kunga vārdu piesauks, taps izglābts.
14 To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
Kā lai nu To piesauc, uz ko nav ticējuši? Bet kā lai tic, par ko nav dzirdējuši? Bet kā lai dzird bez sludinātāja?
15 Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
Bet kā lai sludina, ja netop sūtīti? Itin kā ir rakstīts: cik jaukas ir to prieka vēstnešu kājas, kas sludina mieru, kas sludina labumu.
16 Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
Bet ne visi tam evaņģēlijam bijuši paklausīgi; jo Jesaja saka: Kungs, kas tic mūsu sludināšanai?
17 Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
Tad nu ticība ir no sludināšanas, un sludināšana caur Dieva vārdu.
18 Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
Bet es saku: vai tie nav dzirdējuši? Tiešām, viņu skaņa ir izgājusi pa visu zemi, un viņu vārdi līdz pasaules galam.
19 Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
Bet es saku: vai Israēls to nav sapratis? Jau Mozus saka: “Es jūs kaitināt kaitināšu caur tautu, kas nav Mana, caur ģeķīgu tautu Es jūs tirināt tirināšu.”
20 Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
Bet Jesaja drīkst sacīt: “Es esmu atrasts no tiem, kas Mani nav meklējuši, un esmu tiem parādījies, kas pēc Manis nav vaicājuši.”
21 Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”
Bet uz Israēli viņš saka: “Augu dienu Savas rokas esmu izstiepis pār ļaudīm, kas neklausa, bet runā pretī.”