< Romawa 10 >

1 ’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
Brethren, the will of my heart, indeed, and my prayer to God, is for them unto salvation.
2 Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
For I bear them witness, that they have a zeal of God, but not according to knowledge.
3 Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
For they, not knowing the justice of God, and seeking to establish their own, have not submitted themselves to the justice of God.
4 Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
For the end of the law is Christ, unto justice to every one that believeth.
5 Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
For Moses wrote, that the justice which is of the law, the man that shall do it, shall live by it.
6 Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
But the justice which is of faith, speaketh thus: Say not in thy heart, Who shall ascend into heaven? that is, to bring Christ down;
7 “ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
Or who shall descend into the deep? that is, to bring up Christ again from the dead. (Abyssos g12)
8 Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
But what saith the scripture? The word is nigh thee, even in thy mouth, and in thy heart. This is the word of faith, which we preach.
9 Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
For if thou confess with thy mouth the Lord Jesus, and believe in thy heart that God hath raised him up from the dead, thou shalt be saved.
10 Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
For, with the heart, we believe unto justice; but, with the mouth, confession is made unto salvation.
11 Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
For the scripture saith: Whosoever believeth in him, shall not be confounded.
12 Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
For there is no distinction of the Jew and the Greek: for the same is Lord over all, rich unto all that call upon him.
13 gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
For whosoever shall call upon the name of the Lord, shall be saved.
14 To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
How then shall they call on him, in whom they have not believed? Or how shall they believe him, of whom they have not heard? And how shall they hear, without a preacher?
15 Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
And how shall they preach unless they be sent, as it is written: How beautiful are the feet of them that preach the gospel of peace, of them that bring glad tidings of good things!
16 Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
But all do not obey the gospel. For Isaias saith: Lord, who hath believed our report?
17 Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
Faith then cometh by hearing; and hearing by the word of Christ.
18 Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
But I say: Have they not heard? Yes, verily, their sound hath gone forth into all the earth, and their words unto the ends of the whole world.
19 Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
But I say: Hath not Israel known? First, Moses saith: I will provoke you to jealousy by that which is not a nation; by a foolish nation I will anger you.
20 Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
But Isaias is bold, and saith: I was found by them that did not seek me: I appeared openly to them that asked not after me.
21 Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”
But to Israel he saith: All the day long have I spread my hands to a people that believeth not, and contradicteth me.

< Romawa 10 >