< Romawa 10 >

1 ’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
Bratří, příchylnost zajisté s zvláštní líbostí srdce mého jestiť k Izraelovi, i modlitba za něj k Bohu, aby spasen byl.
2 Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
Neboť jim svědectví vydávám, žeť horlivost Boží mají, ale ne podlé umění.
3 Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
Nebo neznajíce Boží spravedlnosti, a svou vlastní spravedlnost usilujíce vystaviti, spravedlnosti Boží nebyli poddáni.
4 Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
Konec zajisté zákona jest Kristus k ospravedlnění všelikému věřícímu.
5 Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
Nebo Mojžíš píše o spravedlnosti, kteráž jest z zákona, pravě: Který by koli člověk činil ty věci, živ bude v nich.
6 Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
Ta pak spravedlnost, kteráž jest z víry, takto praví: Neříkej v srdci svém: Kdo vstoupí na nebe? To jest Krista s výsosti svésti.
7 “ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
Aneb kdo sstoupí do propasti? To jest Krista z mrtvých vzbuditi. (Abyssos g12)
8 Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
Ale co dí? Blízko tebe jestiť slovo, v ústech tvých a v srdci tvém. Toť jest slovo to víry, kteréž kážeme:
9 Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
Vyznáš-li ústy svými Pána Ježíše, a srdcem svým uvěříš-li, že jej Bůh vzkřísil z mrtvých, spasen budeš.
10 Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
Srdcem se zajisté věří k spravedlnosti, ale ústy vyznání se děje k spasení.
11 Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
Nebo dí písmo: Všeliký, kdož věří v něj, nebude zahanben.
12 Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
Neníť zajisté rozdílu mezi Židem a Řekem; nebo tentýž Pán všech, bohatý jest ke všechněm vzývajícím jej.
13 gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
Každý zajisté, kdožkoli vzýval by jméno Páně, spasen bude.
14 To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
Ale kterak budou vzývati toho, v kteréhož neuvěřili? A kterak uvěří tomu, o němž neslyšeli? A kterak uslyší bez kazatele?
15 Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
A kterak kázati budou, jestliže nebudou posláni? Jakož psáno jest: Jak krásné nohy zvěstujících pokoj, zvěstujících dobré věci.
16 Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
Ale nevšickni uposlechli evangelium. Nebo Izaiáš praví: Pane, kdo uvěřil kázaní našemu?
17 Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
Tedy víra z slyšení, slyšení pak skrze slovo Boží.
18 Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
Ale pravímť: Zdaliž neslyšeli? Anobrž po vší zemi rozšel se zvuk jejich, a do končin okršlku země slova jejich.
19 Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
Ale pravím: Zdaliž nepoznal Izrael? Ano první Mojžíš řekl: Já k závisti vás přivedu skrze národ ten, kterýž není národ; skrze národ nemoudrý k hněvu popudím vás.
20 Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
A Izaiáš směle dí: Nalezen jsem od těch, kteříž mne nehledali; zjeven jsem těm, kteříž se na mne neptali.
21 Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”
Ale proti Izraelovi dí: Přes celý den roztahoval jsem ruce své k lidu nepovolnému a protivnému.

< Romawa 10 >