< Romawa 1 >

1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Павло, раб Ісуса Христа, покликаний [бути] апостолом і обраний, щоб звіщати Добру Звістку Бога,
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
яку Він сповістив раніше через Своїх пророків у Святих Писаннях.
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
Це [Звістка] про Його Сина, Який за тілом був нащадком Давида,
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
а за Духом святості був визнаний Сином Божим у силі через воскресіння з мертвих, – про Ісуса Христа, Господа нашого.
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
Через Нього ми отримали благодать і апостольство, щоб заради Його імені [привести] до послуху віри всі народи,
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
серед яких і ви, покликані Ісуса Христа.
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Усім, хто в Римі, улюбленим Божим, покликаним святим. Благодать вам і мир від Бога, нашого Отця, і від Господа Ісуса Христа.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
Насамперед я дякую моєму Богові через Ісуса Христа за всіх вас, бо про вашу віру говорять у всьому світі.
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
Бог, Якому я служу моїм духом, звіщаючи Добру Звістку Його Сина, є моїм свідком, що я завжди пам’ятаю про вас і
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
постійно прошу у своїх молитвах, щоби з волі Божої мені вдалося нарешті прийти до вас.
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
Прагну побачити вас, щоб розділити з вами якийсь духовний дар для вашого зміцнення,
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
щоб ми підбадьорили одне одного своєю спільною вірою – вашою й моєю.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
Не хочу, брати, щоб ви не знали, як багато разів я планував прийти до вас, аби мати якийсь плід серед вас, як і серед інших народів, але досі мав перешкоди.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
Я боржник перед еллінами й варварами, перед мудрими й неосвіченими.
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
Саме тому я прагну звіщати Добру Звістку і вам у Римі.
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
Я не соромлюся Доброї Звістки Христа, оскільки вона є силою Божою для спасіння кожного, хто вірить, – спочатку юдея, а потім і язичника.
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Адже в ній відкривається праведність Божа з віри у віру, як написано: «А праведник житиме вірою».
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
Бо гнів Божий відкривається з неба проти усякої безбожності та неправедності людей, які своєю неправедністю придушують істину.
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
Бо те, що можна знати про Бога, очевидно для них, адже Бог відкрив їм.
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
Від створення світу невидимі якості Бога – Його вічна сила й божественна природа – були чітко зрозумілі у творінні, так що [люди] не мають виправдання, (aïdios g126)
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
оскільки вони, знаючи Бога, не прославили Його як Бога й не дякували Йому, але їхні думки стали марними, а їхні нерозумні серця охопила темрява.
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Називаючи себе мудрими, вони стали нерозумними
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
й проміняли славу нетлінного Бога на образи, подібні до смертної людини, птахів, тварин і плазунів.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Тому Бог віддав їх у гріховні бажання їхніх нечистих сердець, щоб вони самі між собою осквернили свої тіла.
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
Вони проміняли Божу істину на неправду та поклонялися й служили творінню, а не Творцеві, Який є навіки благословенний. Амінь. (aiōn g165)
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
Через це Бог віддав їх ганебним бажанням. Їхні жінки проміняли природні стосунки на неприродні.
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
Так само й чоловіки відмовилися від природних стосунків із жінками й розпалилися пристрастю один до одного. Чоловіки з чоловіками роблять безсоромні вчинки й отримують самі в собі належне покарання за свої збочення.
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
Оскільки вони не вважали за потрібне пізнати Бога, то Бог віддав їх [їхньому] розпусному розуму, щоб вони робили те, чого не годиться робити.
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
Вони сповнені всякої неправди, зла, жадібності та розпусти, сповнені заздрощів, убивств, чвар, обману та злоби. Вони поширюють плітки та
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
наклепи, ненавидять Бога, вони нахабні, зарозумілі та хвалькуваті, вигадують, як зробити зло, не шанують батьків.
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
У них немає розуміння, вони не виконують обіцянок, не мають любові та милосердя.
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
Хоча вони знають праведний наказ Божий про те, що всі, хто робить такі речі, заслуговують на смерть, вони не тільки продовжують їх робити, але й схвалюють тих, хто [це] робить.

< Romawa 1 >