< Romawa 1 >

1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Paul, serviteur de Jésus-Christ, élu apôtre choisi pour prêcher l'évangile de Dieu,
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
(Évangile promis d'avance par ses prophètes dans les saintes Écritures
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
et concernant son Fils né, quant à la chair, de la race de David,
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
et, quant à l'Esprit de sainteté, déclaré avec puissance Fils de Dieu, par sa résurrection d'entre les morts, Jésus-Christ notre Seigneur);
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
(Nous avons reçu de sa grâce la mission d'amener en son nom à l’obéissance de la foi tous les païens),
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
(dont vous faites aussi partie, vous élus de Jésus-Christ).
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
A tous les biens-aimés de Dieu, fidèles élus qui sont à Rome. Grâce et paix vous soient accordées par Dieu notre Père et par le Seigneur Jésus-Christ.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
Je commence en rendant grâces pour vous tous à mon Dieu par Jésus-Christ de ce que votre foi est renommée dans le monde entier.
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
Le Dieu, que je sers de toute mon âme en prêchant l'Évangile de son Fils, m'est témoin que sans cesse je fais mention de vous dans mes prières,
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
lui demandant toujours que je puisse une fois enfin réussir, par sa volonté, à venir chez vous.
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
J'ai, en effet, le plus grand désir de vous voir, pour vous communiquer quelque don spirituel propre à vous affermir;
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
je veux dire, pour que, chez vous, nous nous encouragions mutuellement, vous et moi, par la foi qui nous est commune.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
Je ne veux pas vous laisser ignorer, mes frères, que souvent j'ai formé le projet d'aller chez vous (j'en ai été empêché jusqu'à présent), afin de recueillir aussi quelques fruits parmi vous comme parmi les autres païens.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
Je me dois aux Grecs et aux étrangers, aux savants et aux ignorants.
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
J'ai donc, pour ma part, grande envie de vous prêcher l'Évangile à vous aussi, habitants de Rome!
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
Car je n'ai pas honte de l'Évangile; il est une puissance de Dieu donnant le salut à tout croyant, au Juif d'abord, puis au païen.
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Il s'y révèle, en effet, une justice de Dieu, qui vient de la foi, qui est accordée à la foi, comme il est écrit: «Le juste vivra par la foi.»
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
Il y a une colère de Dieu qui se révèle du haut du ciel contre toute impiété et toute iniquité d'hommes qui méchamment étouffent la vérité,
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
car ce qu'on peut savoir sur Dieu est à leur portée, Dieu le leur a fait connaître.
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
En effet, les perfections invisibles de Dieu, son éternelle puissance et sa divinité, éclatent aux yeux depuis la création du monde, pour quiconque sait regarder ses oeuvres. De la sorte ils sont inexcusables; (aïdios g126)
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
car enfin, ayant conscience de Dieu, ils ne lui ont ni rendu gloire, ni rendu grâces comme à leur Dieu; au contraire, ils se sont perdus dans des raisonnements sans valeur; leur coeur inintelligent a été plongé dans les ténèbres.
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Ils se sont dits sages et ils ont été insensés,
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
ils ont substitué, à la gloire du Dieu immortel des images représentant l'homme mortel, les oiseaux, les quadrupèdes, les reptiles.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Voilà pourquoi Dieu les a livrés à toutes les passions de leurs coeurs et à une impureté telle qu'eux-mêmes ils déshonorent leurs corps.
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
Oui, c'est pour avoir substitué à la vérité de Dieu le mensonge, pour avoir servi, avoir adoré la créature au lieu du Créateur, — (Béni soit-il à jamais! Amen!) — (aiōn g165)
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
c'est pour cela que Dieu les a livrés à des passions infâmes: Les femmes ont remplacé les relations naturelles par des actes contre nature;
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
les hommes de même ont abandonné leurs relations naturelles avec la femme, se sont pris de passions furieuses les uns pour les autres, ont commis entre hommes des infamies et ont reçu en leurs personnes le salaire que mérite leur égarement;
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
et comme ils ne se sont pas souciés de savoir qui était Dieu, Dieu les a livrés à un esprit d'aveuglement, et ils font ce qu'il ne faut pas faire.
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
Ils ont tous les vices, toutes les méchancetés, toutes les malices, toutes les rapacités; ne respirant qu'envie, meurtre, discorde, ruse, mauvaise foi; délateurs,
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
calomniateurs, impies, insolents, orgueilleux, présomptueux, ingénieux au mal, enfants rebelles,
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
inintelligents, parjures, durs, impitoyables.
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
Ces gens-là connaissent le décret de Dieu qui condamne à mort ceux qui commettent de tels actes, et non seulement ils les commettent, mais ils approuvent ceux qui s'y livrent.

< Romawa 1 >