< Romawa 1 >
1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Paul a servant of Christ Jesus a called apostle set apart for [the] gospel of God,
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
which He promised beforehand through the prophets of Him in [the] Scriptures Holy
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
concerning the Son of Him, who having come of [the] seed of David according to flesh,
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
who having been declared Son of God in power according to [the] Spirit of holiness by resurrection [from the] dead, Jesus Christ the Lord of us,
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
through whom we have received grace and apostleship unto obedience of faith among all the Gentiles on behalf of the name of Him,
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
among whom are also you yourselves called of Jesus Christ;
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
To all those being in Rome beloved of God to [those] called saints: Grace to you and peace from God [the] Father of us and [the] Lord Jesus Christ.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
First indeed I thank the God of mine through Jesus Christ (for *N(k)O*) all of you because the faith of you is being proclaimed in all the world;
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
Witness for me is God, whom I serve in the spirit of mine in the gospel of the Son of Him, how unceasingly mention of you I make always upon the prayers of mine
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
imploring, if somehow now at last I will succeed by the will of God to come to you;
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
I long for to see you, that some I may impart gift to you spiritual to the strengthening of you,
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
that now is to be encouraged together among you through the among one another faith of you both and of me.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
Not I do want now you to be ignorant, brothers, that many times I purposed to come to you and was hindered until the present, that some fruit I may have also among you even as even among the other Gentiles.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
To Greeks both and to barbarians, to [the] wise both and to [the] foolish a debtor I am;
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
Thus as to me myself [there is] readiness also to you who [are] in Rome to evangelise.
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
Not for I am ashamed of the gospel (of the Christ; *K*) [the] power for of God it is unto salvation to everyone who is believing — to Jew both first and to Greek.
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
[The] righteousness for of God in it is revealed from faith to faith even as it has been written: And the righteous by faith will live.
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
Is revealed for [the] wrath of God from heaven upon all ungodliness and unrighteousness of men the truth by unrighteousness suppressing,
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
because the known of God manifest is among them; God for to them has revealed [it].
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios )
The for invisible qualities of Him from [the] creation of [the] world by the things made being understood are clearly seen, the both eternal of Him power and divinity, for to be them without excuse. (aïdios )
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
For having known God not as God they glorified [Him] or were thankful, but they became futile in the thinking of them, and was darkened the foolish of them heart;
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Professing to be wise they became fools
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
and they changed the glory of the immortal God into a likeness of an image of mortal man and birds and quadrupeds and creeping things.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Therefore (and *k*) gave up them God in the desires of the hearts of them to impurity to dishonor the bodies of them between (themselves, *N(k)O*)
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn )
who changed the truth of God into the falsehood, and they reverenced and they served the created thing beyond the [One] having created [it], who is blessed to the ages! Amen. (aiōn )
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
Because of this gave up them God to passions of dishonor; Even for females of them changed the natural use into that contrary to nature,
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
Likewise then also the males having left the natural use of the female were inflamed in the desire of them toward one another, males with males the shame working out, and the recompense which was fitting of the error of them in themselves receiving.
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
And even as not they did see fit God to have in [their] knowledge, gave up them God to a depraved mind to do the [things] not being proper,
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
filled with all unrighteousness (sexual immorality *K*) wickedness, covetousness, malice, full of envy, murder, strife, deceit, maliciousness, gossips
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
slanderers, hateful to God, insolent arrogant, boastful, inventors of evil things, to parents disobedient,
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
foolish, untrustworthy, heartless (implacable, *K*) unmerciful,
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
who the righteous decree of God having known that those such things doing worthy of death are, not only them they are practicing but also they are approving of those practicing [them].