< Romawa 1 >

1 Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
Pavel, služebník Jezukristův, povolaný apoštol, oddělený k kázaní evangelium Božího,
2 Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
Kteréž zdávna zaslíbil skrze proroky své v písmích svatých,
3 game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
O Synu svém zplozeném z semene Davidova s strany těla,
4 Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
Kterýž prokázán jest býti Synem Božím mocně, podlé Ducha posvěcení, skrze z mrtvých vstání, totiž o Ježíši Kristu, Pánu našem,
5 Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
Skrze něhož jsme přijali milost a apoštolství ku poslušenství víry mezi všemi národy pro jméno jeho,
6 Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
Z nichž i vy jste povolaní Ježíše Krista,
7 Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Všechněm, kteříž jste v Římě, milým Božím, povolaným svatým: Milost vám a pokoj od Boha Otce našeho a Pána Ježíše Krista.
8 Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
Nejprvé pak díky činím Bohu svému skrze Ježíše Krista ze všech vás, že víra vaše rozhlašuje se po všem světě.
9 Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
Svědek mi jest zajisté Bůh, kterémuž sloužím duchem svým v evangelium Syna jeho, žeť bez přestání zmínku o vás činím,
10 cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
Vždycky na svých modlitbách žádaje, abych aspoň někdy mohl šťastně, byla-li by vůle Boží, k vám přijíti.
11 Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
Neboť velice žádám viděti vás, abych vám udělil částku nějakou milosti duchovní ku potvrzení vašemu,
12 wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
To jest, abych spolu s vámi potěšen byl, skrze společnou i vaši i mou víru.
13 Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
Nechciť pak, bratří, abyste nevěděli, žeť jsem mnohokrát uložil přijíti k vám, (ale překážky jsem měl až dosavad, ) abych nějaký užitek také i mezi vámi měl, jako i mezi jinými národy.
14 Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
Nebo Řeků i kterýchkoli jiných národů, i moudrých i nemoudrých, dlužník jsem.
15 Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
A tak, pokudž na mně jest, hotov jsem i vám, kteříž v Římě jste, zvěstovati evangelium.
16 Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
Neboť se nestydím za evangelium Kristovo; moc zajisté Boží jest k spasení každému věřícímu, Židu předně, potom i Řeku.
17 Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
Nebo spravedlnost Boží zjevuje se skrze ně z víry u víru, jakož psáno jest: Spravedlivý pak z víry živ bude.
18 Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
Zjevuje se zajisté hněv Boží s nebe proti každé bezbožnosti a nepravosti lidí, pravdu Boží v nepravosti zadržujících.
19 gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
Nebo což poznáno býti může o Bohu, známé jest jim, Bůh zajisté zjevil jim.
20 Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
Nebo neviditelné věci jeho, hned od stvoření světa, po věcech učiněných rozumem pochopeny bývají, totiž ta jeho věčná moc a Božství, tak aby oni byli bez výmluvy, (aïdios g126)
21 Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
Proto že poznavše Boha, nectili jako Boha, ani jemu děkovali, ale marní učiněni jsou v myšleních svých, a zatmíno jest nemoudré srdce jejich.
22 Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
Měvše se za moudré, blázni učiněni jsou.
23 suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
Nebo směnili slávu neporušitelného Boha v podobenství obrazu porušitelného člověka, i ptactva, i hovad čtvernohých, i zeměplazů.
24 Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
Protož i Bůh vydal je v žádosti srdce jejich k nečistotě, aby zprznili těla svá vespolek.
25 Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
Jako ty, kteříž směnili pravdu Boží za lež, a ctili i sloužili stvoření raději nežli stvořiteli, kterýž jest požehnaný na věky. Amen. (aiōn g165)
26 Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
Protož je vydal Bůh v žádosti ohavné. Nebo i ženy jejich změnily přirozené sebe užívání v to, kteréž jest proti přirození.
27 Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
A podobně i mužské pohlaví, opustivše přirozené užívání ženy, rozpálili se v žádosti své jedni k druhým, mužské pohlaví s mužským pohlavím mrzkost pášíce, a spravedlivou mzdu, kteráž na jejich blud slušela, sami na sebe uvodíce.
28 Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
A jakož sobě nevážili známosti Boha, tak i Bůh vydal je v převrácený smysl, aby činili to, což nesluší,
29 Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
Jsouce naplněni vší nepravostí, smilstvem, nešlechetností, lakomstvím, zlostí, plní závisti, vraždy, svárů, lsti, zlých obyčejů,
30 da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
Utrhači, pomluvači, Boha nenávidící, hánliví, pyšní, chlubní, nalezači zlých věcí, rodičů neposlušní,
31 su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
Nemoudří, smluv nezdrželiví, beze vší lítosti, neukojitelní a nemilosrdní.
32 Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.
Kteříž vědouce o tom právu Božím, (že ti, kteříž takové věci činí, hodni jsou smrti, ) netoliko ty věci činí, ale i činícím nakládají.

< Romawa 1 >