< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
A revelation of Jesus Christ, which God gave to him, to show to his servants the things which must shortly be; and sending by his messenger, he signified them to his servant John,
2 wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
who testified the word of God, and the testimony of Jesus Christ, whatever he saw.
3 Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
Happy is he that reads, and they that hear the words of this prophecy, and keep the things that are written in it; for the time is at hand.
4 Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
John, to the seven congregation which are in Asia; favor and peace be with you, from him who is, and who was, and who is to come; and from the seven spirits which are before his throne;
5 da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
and from Jesus Christ, the faithful witness, the first born of the dead, and the ruler of the kings of the earth; to him who has loved us, and washed us from our sins in his own blood,
6 ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
and has made us kings and priests to his God and Father; to him be glory and dominion for ever and ever. Amen. (aiōn g165)
7 “Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
Behold, he is coming in the clouds; and every eye shall see him, even they who pierced him: and all the tribes of the earth shall mourn because of him. Yes: so let it be.
8 “Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
I am the Alpha and the Omega, says the Lord, who is, and who was, and who is to come, the Almighty.
9 Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
I, John, who am also your brother and companion in tribulation, and in the kingdom and patience of Jesus Christ, was in the island called Patmos, for the sake of the word of God, and for the testimony of Jesus Christ.
10 A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
I was in the Spirit on the Lord's day, and heard a great voice behind me, as of a trumpet,
11 wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
saying, What you see, write in a book, and send it to the seven congregations; to Ephesus, and to Smyrna, and to Pergamos, and to Thyatira, and to Sardis, and to Philadelphia, and to Laodicea.
12 Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
And I turned to see the voice which spoke to me, and being turned, I saw seven golden lamps;
13 A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
and, in the midst of the seven lamps, one like a Son of Man, clothed in a long robe, and girded about the breasts with a golden girdle.
14 Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
His head, even his hairs, were white like wool, as white as snow; and his eyes were as a flame of fire;
15 Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
and his feet like fine brass, when glowing in a furnace; and his voice as the voice of many waters;
16 A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
and he had in his right hand seven stars, and out of his mouth there went a sharp two-edged sword; and his countenance was as the sun, when he shines in his strength.
17 Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
And when I saw him, I fell down at his feet, as dead; and he laid his right hand upon me, and said, Fear not; I am the First and the Last;
18 Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
I am he who lives and was dead; and behold, I am living for ever and ever; and I have the keys of the unseen world, and of death. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 “Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
Write the things which you see, even those which are, and the things which shall be hereafter.
20 Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.
As to the hidden meaning of the seven stars, which you see in my right hand, and of the seven lamps of gold: the seven stars are messengers of the seven congregations; and the seven lamps which you see, are seven congregations.

< Ru’uya ta Yohanna 1 >