< Ru’uya ta Yohanna 9 >

1 Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos g12)
I zatrąbił piąty Anioł i widziałem, że gwiazda spadła z nieba na ziemię, a dano jej klucz studni przepaści. (Abyssos g12)
2 Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos g12)
I otworzyła studnię przepaści; i wystąpił dym z onej studni, jakoby dym pieca wielkiego, i zaćmiło się słońce i powietrze od dymu onej studni. (Abyssos g12)
3 Daga cikin hayaƙin kuwa fāri suka fito zuwa cikin duniya aka kuma ba su iko irin na kunaman duniya.
A z onego dymu wyszły szarańcze na ziemię i dano im moc, jako mają moc niedźwiadki ziemskie;
4 Aka faɗa musu kada su yi wa ciyawa na duniya lahani ko wani tsiro ko itace, sai dai su yi wa mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu kaɗai lahani.
A rzeczono im, żeby nie szkodziły trawie ziemi, ani żadnej rzeczy zielonej, ani żadnemu drzewu, ale tylko samym ludziom, którzy nie mają pieczęci Bożej na czołach swoich.
5 Ba a ba su iko su kashe su ba, sai dai su ba su azaba na watanni biyar. Azabar da suka sha kuwa ya yi kamar ta harbin kunama sa’ad da ta harbi mutum.
A dano im, nie żeby ich zabijały, ale aby ich dręczyły przez pięć miesięcy, a udręczenie ich, aby było jako udręczenie od niedźwiadka, gdy człowieka ukąsi.
6 Cikin waɗannan kwanakin mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su samu ba; za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za tă ɓace musu.
Przetoż w one dni szukać będą ludzie śmierci, ale jej nie znajdą; i będą chcieli umrzeć, ale śmierć od nich uciecze.
7 Kamannin fārin nan kuwa yana kama da dawakan da aka shirya don yaƙi. A kawunansu kuwa da wani abu da ya yi kamar rawanin zinariya, fuskokinsu kuma sun yi kamar fuskokin mutane.
A kształt onych szarańczy podobny był koniom zgotowanym do bitwy, a na głowach ich były jakoby korony podobne złotu, a twarze ich jako twarze ludzkie;
8 Gashin kansu ya yi kamar gashin kan mata, haƙoransu kuma sun yi kamar haƙoran zakoki.
I miały włosy jako włosy niewieście, a zęby ich były jako lwie;
9 Suna da sulkuna kamar sulkunan ƙarfe, ƙarar fikafikansu kuma ta yi kamar motsin dawakai da kekunan yaƙi masu yawa da suke rugawa zuwa yaƙi.
A miały pancerze jako pancerze żelazne, a szum skrzydeł ich, jako grzmot wozów, gdy wiele koni bieży do bitwy.
10 Suna da wutsiyoyi da ƙari kamar kunamai, kuma a wutsiyoyinsu suna da iko su ba wa mutane azaba na wata biyar.
A ogony miały podobne niedźwiadkom, a żądła były w ogonach ich, a moc ich była szkodzić ludziom przez pięć miesięcy;
11 Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos g12)
A miały nad sobą króla, anioła przepaści, któremu imię po żydowsku Abaddon, a po grecku ma imię Apolijon. (Abyssos g12)
12 Bala’i na fari ya wuce, sauran bala’i biyu suna nan zuwa.
Biada jedno przeszło, a oto jeszcze idą dwa biada potem.
13 Mala’ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji murya tana fitowa daga ƙahonin bagaden zinariya da suke a gaban Allah.
Tedy zatrąbił Anioł szósty, a słyszałem głos jeden ze czterech rogów ołtarza złotego, który jest przed oblicznością Bożą,
14 Ta ce wa mala’ika na shida da yake da ƙahon, “Ka saki mala’iku huɗun nan da suke a daure a babban kogin Yuferites.”
Mówiący szóstemu Aniołowi, który miał trąbę: Rozwiąż onych czterech Aniołów związanych u wielkiej rzeki Eufrates.
15 Mala’iku huɗun nan kuwa da aka shirya musamman don wannan sa’a da kuma don wannan rana da wata da kuma shekara aka sake su domin su kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam.
I rozwiązani są oni czterej Aniołowie, zgotowani na godzinę i na dzień, i na miesiąc, i na rok, aby pobili trzecią część ludzi.
16 Yawan rundunan masu hawan dawakan nan mutum miliyon ɗari biyu ne. Na ji adadinsu.
A liczba wojska jezdnego była dwieściekroć tysiąc tysięcy; bom słyszał liczbę ich.
17 Dawakai da masu hawansu da na gani cikin wahayina sun yi kamar. Sulkunansu ja wur ne, baƙin shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta. Kawunan dawakan sun yi kamar kawunan zakoki, daga bakunansu kuwa wuta, hayaƙi, da farar wuta suna fitowa.
Widziałem także konie w widzeniu, a ci, którzy siedzieli na nich, mieli pancerze ogniste hijacyntowe i siarczane; a głowy onych koni były jako głowy lwie, a z gęby ich wychodził ogień i dym i siarka.
18 Aka kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam da annobai uku na wuta, hayaƙi da farar wuta da suka fito daga bakunansu.
A od tego trojga pobita jest trzecia część ludzi od ognia i od dymu, i od siarki, które wychodziły z gąb ich.
19 Ƙarfin dawakan nan kuwa yana a bakunansu da wutsiyoyinsu; gama wutsiyoyinsu suna kama da macizai masu kawuna, da wutsiyoyin ne kuma suke yi wa mutane rauni.
Albowiem moc ich jest w gębach ich i w ogonach ich; bo ogony ich wężom są podobne, mając głowy, któremi szkodzą.
20 Sauran’yan Adam da ba a kashe ta wajen waɗannan annobai ba kuwa har wa yau ba su tuba daga aikin hannuwansu ba; ba su daina bauta wa aljanu, da gumakan zinariya, azurfa, tagulla, dutse da na itace, gumakan da ba sa iya gani ko ji ko tafiya ba.
A inni ludzie, którzy nie są pobici temi plagami, ani pokutowali od uczynków rąk swoich, aby się nie kłaniali dyjabłom i bałwanom złotym i srebrnym, i miedzianym, i kamiennym i drewnianym, którzy ani widzieć nie mogą, ani słyszeć, ani chodzić;
21 Ba su kuma tuba daga kisankansu, sihirinsu, fasikancinsu ko kuma daga sace-sacensu ba.
Ani pokutowali z mężobójstw swoich, ani z czarów swoich, ani z wszeteczeństw swoich, ani z złodziejstw swoich.

< Ru’uya ta Yohanna 9 >