< Ru’uya ta Yohanna 9 >

1 Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos g12)
The fifth angel blew his trumpet; and I saw a Star which had fallen from Heaven to the earth; and to him was given the key of the depths of the bottomless pit, (Abyssos g12)
2 Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos g12)
and he opened the depths of the bottomless pit. And smoke came up out of the pit resembling the smoke of a vast furnace, so that the sun was darkened, and the air also, by reason of the smoke of the pit. (Abyssos g12)
3 Daga cikin hayaƙin kuwa fāri suka fito zuwa cikin duniya aka kuma ba su iko irin na kunaman duniya.
And from the midst of the smoke there came locusts on to the earth, and power was given to them resembling the power which earthly scorpions possess.
4 Aka faɗa musu kada su yi wa ciyawa na duniya lahani ko wani tsiro ko itace, sai dai su yi wa mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu kaɗai lahani.
And they were forbidden to injure the herbage of the earth, or any green thing, or any tree. They were only to injure human beings--those who have not the seal of God on their foreheads.
5 Ba a ba su iko su kashe su ba, sai dai su ba su azaba na watanni biyar. Azabar da suka sha kuwa ya yi kamar ta harbin kunama sa’ad da ta harbi mutum.
Their mission was not to kill, but to cause awful agony for five months; and this agony was like that which a scorpion inflicts when it stings a man.
6 Cikin waɗannan kwanakin mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su samu ba; za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za tă ɓace musu.
And at that time people will seek death, but will by no possibility find it, and will long to die, but death evades them.
7 Kamannin fārin nan kuwa yana kama da dawakan da aka shirya don yaƙi. A kawunansu kuwa da wani abu da ya yi kamar rawanin zinariya, fuskokinsu kuma sun yi kamar fuskokin mutane.
The appearance of the locusts was like that of horses equipped for war. On their heads they had wreaths which looked like gold.
8 Gashin kansu ya yi kamar gashin kan mata, haƙoransu kuma sun yi kamar haƙoran zakoki.
Their faces seemed human and they had hair like women's hair, but their teeth resembled those of lions.
9 Suna da sulkuna kamar sulkunan ƙarfe, ƙarar fikafikansu kuma ta yi kamar motsin dawakai da kekunan yaƙi masu yawa da suke rugawa zuwa yaƙi.
They had breast-plates which seemed to be made of steel; and the noise caused by their wings was like that of a vast number of horses and chariots hurrying into battle.
10 Suna da wutsiyoyi da ƙari kamar kunamai, kuma a wutsiyoyinsu suna da iko su ba wa mutane azaba na wata biyar.
They had tails like those of scorpions, and also stings; and in their tails lay their power of injuring mankind for five months.
11 Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos g12)
The locusts had a king over them--the angel of the bottomless pit, whose name in Hebrew is 'Abaddon,' while in the Greek he is called 'Apollyon.' (Abyssos g12)
12 Bala’i na fari ya wuce, sauran bala’i biyu suna nan zuwa.
The first woe is past; two other woes have still to come.
13 Mala’ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji murya tana fitowa daga ƙahonin bagaden zinariya da suke a gaban Allah.
The sixth angel blew his trumpet; and I heard a single voice speaking from among the horns of the golden incense altar which is in the presence of God.
14 Ta ce wa mala’ika na shida da yake da ƙahon, “Ka saki mala’iku huɗun nan da suke a daure a babban kogin Yuferites.”
It said to the sixth angel--the angel who had the trumpet, "Set at liberty the four angels who are prisoners near the great river Euphrates."
15 Mala’iku huɗun nan kuwa da aka shirya musamman don wannan sa’a da kuma don wannan rana da wata da kuma shekara aka sake su domin su kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam.
And the four angels who had been kept in readiness for that hour, day, month, and year, were set at liberty, so that they might kill a third part of mankind.
16 Yawan rundunan masu hawan dawakan nan mutum miliyon ɗari biyu ne. Na ji adadinsu.
The number of the cavalry was two hundred millions; I heard their number.
17 Dawakai da masu hawansu da na gani cikin wahayina sun yi kamar. Sulkunansu ja wur ne, baƙin shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta. Kawunan dawakan sun yi kamar kawunan zakoki, daga bakunansu kuwa wuta, hayaƙi, da farar wuta suna fitowa.
And this was the appearance of the horses which I saw in my vision--and of their riders. The body-armour of the riders was red, blue and yellow; and the horses' heads were shaped like the heads of lions, while from their mouths there came fire and smoke and sulphur.
18 Aka kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam da annobai uku na wuta, hayaƙi da farar wuta da suka fito daga bakunansu.
By these three plagues a third part of mankind were destroyed--by the fire and the smoke, and by the sulphur which came from their mouths.
19 Ƙarfin dawakan nan kuwa yana a bakunansu da wutsiyoyinsu; gama wutsiyoyinsu suna kama da macizai masu kawuna, da wutsiyoyin ne kuma suke yi wa mutane rauni.
For the power of the horses is in their mouths and in their tails; their tails being like serpents, and having heads, and it is with them that they inflict injury.
20 Sauran’yan Adam da ba a kashe ta wajen waɗannan annobai ba kuwa har wa yau ba su tuba daga aikin hannuwansu ba; ba su daina bauta wa aljanu, da gumakan zinariya, azurfa, tagulla, dutse da na itace, gumakan da ba sa iya gani ko ji ko tafiya ba.
But the rest of mankind who were not killed by these plagues, did not even then repent and leave the things they had made, so as to cease worshipping the demons, and the idols of gold and silver, bronze, stone, and wood, which can neither see nor hear, nor move.
21 Ba su kuma tuba daga kisankansu, sihirinsu, fasikancinsu ko kuma daga sace-sacensu ba.
Nor did they repent of their murders, their practice of magic, their fornication, or their thefts.

< Ru’uya ta Yohanna 9 >