< Ru’uya ta Yohanna 9 >

1 Mala’ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga tauraron da ya fāɗo duniya daga sararin sama. Aka ba wa tauraron mabuɗin ramin Abis. (Abyssos g12)
And the fifth angel sounded; and I saw a star fall from heaven to the earth; and there was given to him the key of the pit of the abyss; (Abyssos g12)
2 Da ya buɗe Abis ɗin, sai hayaƙi ya taso daga cikin kamar hayaƙin matoya mai girma. Hayaƙin nan daga Abis ya duhunta rana da sararin sama. (Abyssos g12)
and he opened the pit of the abyss; and there arose a smoke out of the pit, like the smoke of a great furnace; and the sun and the air were darkened by the smoke of the pit. (Abyssos g12)
3 Daga cikin hayaƙin kuwa fāri suka fito zuwa cikin duniya aka kuma ba su iko irin na kunaman duniya.
And out of the smoke there came locusts upon the earth; and power was given to them, as the scorpions of the earth have power.
4 Aka faɗa musu kada su yi wa ciyawa na duniya lahani ko wani tsiro ko itace, sai dai su yi wa mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu kaɗai lahani.
And they were commanded not to hurt the grass of the earth, nor any green thing, nor any tree, but the men who have not the seal of God in their foreheads.
5 Ba a ba su iko su kashe su ba, sai dai su ba su azaba na watanni biyar. Azabar da suka sha kuwa ya yi kamar ta harbin kunama sa’ad da ta harbi mutum.
And they were permitted, not to kill them, but to torment them five months; and the torment inflicted by them was like the torment inflicted by a scorpion, when he stings a man.
6 Cikin waɗannan kwanakin mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su samu ba; za su yi marmarin mutuwa, amma mutuwa za tă ɓace musu.
And in those days men will seek for death, and shall not find it; and they will desire to die, and death shall flee from them.
7 Kamannin fārin nan kuwa yana kama da dawakan da aka shirya don yaƙi. A kawunansu kuwa da wani abu da ya yi kamar rawanin zinariya, fuskokinsu kuma sun yi kamar fuskokin mutane.
And the shapes of the locusts were like horses prepared for battle; and on their heads were, as it were, crowns of gold; and their faces were like the faces of men.
8 Gashin kansu ya yi kamar gashin kan mata, haƙoransu kuma sun yi kamar haƙoran zakoki.
And they had hair like the hair of women; and their teeth were like the teeth of lions.
9 Suna da sulkuna kamar sulkunan ƙarfe, ƙarar fikafikansu kuma ta yi kamar motsin dawakai da kekunan yaƙi masu yawa da suke rugawa zuwa yaƙi.
And they had breastplates like breastplates of iron; and the sound of their wings was like the sound of chariots of many horses running to battle.
10 Suna da wutsiyoyi da ƙari kamar kunamai, kuma a wutsiyoyinsu suna da iko su ba wa mutane azaba na wata biyar.
And they had tails like scorpions, and there were stings in their tails; and they had power to hurt men five months.
11 Suna da sarkin da yake mulki a bisansu wanda yake mala’ikan Abis, wanda sunansa a harshen Yahudawa shi ne Abaddon, da harshen Hellenawa kuwa shi ne, Afolliyon. (Abyssos g12)
And they had over them a king, the angel of the abyss: his name, in Hebrew, is Abaddon, and, in Greek, he has the name Apollyon. (Abyssos g12)
12 Bala’i na fari ya wuce, sauran bala’i biyu suna nan zuwa.
The first woe is past: behold, there are coming, after this, two woes more.
13 Mala’ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji murya tana fitowa daga ƙahonin bagaden zinariya da suke a gaban Allah.
And the sixth angel sounded: and I heard a voice from the four horns of the golden altar that is before God,
14 Ta ce wa mala’ika na shida da yake da ƙahon, “Ka saki mala’iku huɗun nan da suke a daure a babban kogin Yuferites.”
saying to the sixth angel, who had the trumpet: Loose the four angels that are bound at the great river Euphrates.
15 Mala’iku huɗun nan kuwa da aka shirya musamman don wannan sa’a da kuma don wannan rana da wata da kuma shekara aka sake su domin su kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam.
And the four angels were loosed, who were prepared for an hour, and a day, and a month, and a year, to slay the third part of men.
16 Yawan rundunan masu hawan dawakan nan mutum miliyon ɗari biyu ne. Na ji adadinsu.
And the number of the armies of horsemen was two myriads of myriads: I heard the number of them.
17 Dawakai da masu hawansu da na gani cikin wahayina sun yi kamar. Sulkunansu ja wur ne, baƙin shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta. Kawunan dawakan sun yi kamar kawunan zakoki, daga bakunansu kuwa wuta, hayaƙi, da farar wuta suna fitowa.
And thus I saw the horses in the vision, and those who sat on them; they had breastplates, fiery, and hyacinthine, and sulphurous: and the heads of the horses were like the heads of lions, and out of their mouths issued fire and smoke and brimstone.
18 Aka kashe kashi ɗaya bisa uku na’yan Adam da annobai uku na wuta, hayaƙi da farar wuta da suka fito daga bakunansu.
By these three plagues was the third part of men killed, by the fire, and the smoke, and the brimstone that issued out of their mouths.
19 Ƙarfin dawakan nan kuwa yana a bakunansu da wutsiyoyinsu; gama wutsiyoyinsu suna kama da macizai masu kawuna, da wutsiyoyin ne kuma suke yi wa mutane rauni.
For their power was in their mouth and in their tails; for their tails were like serpents, and had heads, and with them they do injury.
20 Sauran’yan Adam da ba a kashe ta wajen waɗannan annobai ba kuwa har wa yau ba su tuba daga aikin hannuwansu ba; ba su daina bauta wa aljanu, da gumakan zinariya, azurfa, tagulla, dutse da na itace, gumakan da ba sa iya gani ko ji ko tafiya ba.
And the rest of men that were not killed by these plagues, repented not of the works of their hands, that they might not worship demons, and idols of gold, and of silver, and of brass, and of stone, and of wood, which can neither see, nor hear, nor walk;
21 Ba su kuma tuba daga kisankansu, sihirinsu, fasikancinsu ko kuma daga sace-sacensu ba.
and they repented not of their murders, nor of their sorceries, nor of their lewdness, nor of their thefts.

< Ru’uya ta Yohanna 9 >