< Ru’uya ta Yohanna 8 >

1 Sa’ad da ya buɗe hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kusan rabin sa’a.
A I kona akaa ana i ka hiku o na wepa, hamau loa ko ka lani e like me ka hapalua hora.
2 Sai na ga mala’iku bakwai da suke tsayawa a gaban Allah, a gare su kuwa aka ba da ƙahoni bakwai.
A ike aku la au i na anela ehiku, ka poe i ku imua o ke Akua; a ua Laawiia mai ia lakou ehiku pu puhi.
3 Wani mala’ika, da yake da kaskon zinariyar da ake zuba turare, ya zo ya tsaya kusa da bagaden. Aka ba shi turare da yawa don yă miƙa tare da addu’o’in dukan tsarkaka a bisa bagaden zinariya a gaban kursiyin.
A hele ae la kekahi anela hou, a ku mai la ma ke kuahu, he ipuala gula kana; a ua haawiia mai he mea ala ia ia he nui loa, i amama pu oia ia mea me na pule a ka poe haipule a pau, ma ka lele gula aia imua o ka nohoalii.
4 Hayaƙin turaren tare da addu’o’in tsarkaka, suka hau zuwa gaban Allah daga hannun mala’ikan.
Punohu aku la ka uahi o ia mea ala a me na pule a ka poe haipule, mai ka lima aku o ka anela, imua o ke Akua.
5 Sai mala’ikan ya ɗauki kaskon, ya cika shi da wuta daga bagaden, ya kuma wurga shi bisan duniya; sai aka yi ta yin tsawa, ƙararraki, walƙiya, da kuma girgizar ƙasa.
Lawe ae la ka anela i ka ipuala a hahao iho la a piha i ke ahi o ke kuahu, a kiola iho la ilalo i ka honua; alaila puka mai la na leo, a me na hekili, a me na uila, a me ke olai.
6 Sai mala’iku bakwai ɗin nan da suke da ƙahoni bakwai suka shirya don su busa su.
A o na anela ehiku, ia lakou na pu ehiku, hoomakaukau lakou e puhi.
7 Mala’ika na fari ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta haɗe da jini, aka kuma wurga su bisan duniya. Kashi ɗaya bisa uku na duniya ya ƙone, kashi ɗaya bisa uku na itatuwa suka ƙone, dukan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone.
A puhi ae la ka anela mua, a hiki mai la ka hua hekili, a me ke ahi, i hui pu ia me ke koko, ua hooleiia iho la ia i ka honua. Pau iho la i ke ahi ka hapakolu o na laau, a pau no hoi ka mauu uliuli a pau i ke ahi.
8 Mala’ika na biyu ya busa ƙahonsa, sai ga wani abu kamar babban dutse mai cin wuta, aka jefa cikin teku. Kashi ɗaya bisa uku na teku ya zama jini,
A puhi ae la ka anela elua, a ua hooleiia'ku la i ke kai, he mea e like me ke kuahiwi nui e aa ana i ke ahi. A lilo iho la ka hapakolu o ke kai i koko.
9 kashi ɗaya bisa uku na halittu masu rai da suke cikin tekun suka mutu, kashi ɗaya bisa uku kuma na jiragen ruwa kuma suka hallaka.
A make iho la ka hapakolu o na mea e ola ana iloko o ke kai; a lukuia iho la ka hapakolu o na moku.
10 Mala’ika na uku ya busa ƙahonsa, sai wani babban tauraro mai cin wuta kamar toci, ya fāɗi daga sararin sama, a kan kashi ɗaya bisa uku na koguna da kuma a bisa maɓulɓulan ruwa
A puhi ae la ka anela ekolu, a haule mai kekahi hoku nui, mai ka lani mai, e aa ana e like me ka ipukukui, a haule ia maluna o ka hapakolu o na muliwai, a maluna o na wai puna;
11 sunan tauraron kuwa Maɗaci. Kashi ɗaya bisa uku na ruwaye ya zama mai ɗaci, mutane da yawa kuma suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.
Ua kapaia'ku ka inoa o ia hoku o Awaawa; a lilo iho la kekahi hapakolu o na wai i awaawa; a nui loa iho la ka poe kanaka i make i ka wai, no ka mea, ua lilo ia i mea awaawa.
12 Mala’ika na huɗu ya busa ƙahonsa, sai aka bugi kashi ɗaya bisa uku na rana, kashi ɗaya bisa uku na wata, da kashi ɗaya bisa uku na taurari, har kashi ɗaya bisa uku nasu ya duhunta. Kashi ɗaya bisa uku na yini ya kasance babu haske, haka ma kashi ɗaya bisan uku na dare.
A puhi ae la ka anela ha, a ua hahauia'ku la kekahi hapakolu o ka la, a me ka hapakolu o ka mahina, a me ka hapakolu o na hoku; ua poeleele ka hapakolu o lakou, a o ka hapakolu o ke ao, aole malamalama, a pela no hoi ka po.
13 Yayinda nake kallo, sai na ji gaggafar da take tashi sama a tsakiyar sararin sama ta yi kira da babbar murya ta ce, “Kaito! Kaito! Kaiton mazaunan duniya, in an yi busan sauran ƙahonin da mala’ikun nan uku suke shirin busawa!”
Nana aku la au, a lohe aku la i kekahi anela e lele ana mawaena o ka lani, e hea ana me ka leo nui, Auwe, auwe, auwe, i ka poe e noho la ma ka honua, no na kani ana i koe o ka pu o na anela ekolu i makaukau e hookani mai!

< Ru’uya ta Yohanna 8 >