< Ru’uya ta Yohanna 8 >
1 Sa’ad da ya buɗe hatimi na bakwai, sai aka yi shiru a sama na kusan rabin sa’a.
When the Lamb broke the seventh seal, there was silence in Heaven for about half an hour.
2 Sai na ga mala’iku bakwai da suke tsayawa a gaban Allah, a gare su kuwa aka ba da ƙahoni bakwai.
Then I saw the seven angels who are in the presence of God, and seven trumpets were given to them.
3 Wani mala’ika, da yake da kaskon zinariyar da ake zuba turare, ya zo ya tsaya kusa da bagaden. Aka ba shi turare da yawa don yă miƙa tare da addu’o’in dukan tsarkaka a bisa bagaden zinariya a gaban kursiyin.
And another angel came and stood close to the altar, carrying a censer of gold; and abundance of incense was given to him that he might place it with the prayers of all God's people upon the golden altar which was in front of the throne.
4 Hayaƙin turaren tare da addu’o’in tsarkaka, suka hau zuwa gaban Allah daga hannun mala’ikan.
And the smoke of the incense rose into the presence of God from the angel's hand, and mingled with the prayers of His people.
5 Sai mala’ikan ya ɗauki kaskon, ya cika shi da wuta daga bagaden, ya kuma wurga shi bisan duniya; sai aka yi ta yin tsawa, ƙararraki, walƙiya, da kuma girgizar ƙasa.
So the angel took the censer and filled it with fire from the altar and flung it to the earth; and there followed peals of thunder, and voices, and flashes of lightning, and an earthquake.
6 Sai mala’iku bakwai ɗin nan da suke da ƙahoni bakwai suka shirya don su busa su.
Then the seven angels who had the seven trumpets made preparations for blowing them.
7 Mala’ika na fari ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta haɗe da jini, aka kuma wurga su bisan duniya. Kashi ɗaya bisa uku na duniya ya ƙone, kashi ɗaya bisa uku na itatuwa suka ƙone, dukan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone.
The first blew his trumpet; and there came hail and fire, mixed with blood, falling upon the earth; and a third part of the earth was burnt up, and a third part of the trees and all the green grass.
8 Mala’ika na biyu ya busa ƙahonsa, sai ga wani abu kamar babban dutse mai cin wuta, aka jefa cikin teku. Kashi ɗaya bisa uku na teku ya zama jini,
The second angel blew his trumpet; and what seemed to be a great mountain, all ablaze with fire, was hurled into the sea; and a third part of the sea was turned into blood.
9 kashi ɗaya bisa uku na halittu masu rai da suke cikin tekun suka mutu, kashi ɗaya bisa uku kuma na jiragen ruwa kuma suka hallaka.
And a third part of the creatures that were in the sea--those that had life--died; and a third part of the ships were destroyed.
10 Mala’ika na uku ya busa ƙahonsa, sai wani babban tauraro mai cin wuta kamar toci, ya fāɗi daga sararin sama, a kan kashi ɗaya bisa uku na koguna da kuma a bisa maɓulɓulan ruwa
The third angel blew his trumpet; and there fell from Heaven a great star, which was on fire like a torch. It fell upon a third part of the rivers and upon the springs of water.
11 sunan tauraron kuwa Maɗaci. Kashi ɗaya bisa uku na ruwaye ya zama mai ɗaci, mutane da yawa kuma suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa.
The name of the star is 'Wormwood;' and a third part of the waters were turned into wormwood, and vast numbers of the people died from drinking the water, because it had become bitter.
12 Mala’ika na huɗu ya busa ƙahonsa, sai aka bugi kashi ɗaya bisa uku na rana, kashi ɗaya bisa uku na wata, da kashi ɗaya bisa uku na taurari, har kashi ɗaya bisa uku nasu ya duhunta. Kashi ɗaya bisa uku na yini ya kasance babu haske, haka ma kashi ɗaya bisan uku na dare.
Then the fourth angel blew his trumpet; and a curse fell upon a third part of the sun, a third part of the moon, and a third part of the stars, so that a third part of them were darkened and for a third of the day, and also of the night, there was no light.
13 Yayinda nake kallo, sai na ji gaggafar da take tashi sama a tsakiyar sararin sama ta yi kira da babbar murya ta ce, “Kaito! Kaito! Kaiton mazaunan duniya, in an yi busan sauran ƙahonin da mala’ikun nan uku suke shirin busawa!”
Then I looked, and I heard a solitary eagle crying in a loud voice, as it flew across the sky, "Alas, alas, alas, for the inhabitants of the earth, because of the significance of the remaining trumpets which the three angels are about to blow!"