< Ru’uya ta Yohanna 7 >

1 Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
آنگاه چهار فرشته دیدم که در چهار گوشهٔ زمین ایستاده‌اند و نمی‌گذارند بادهای چهارگانه بر زمین بوزند، تا دیگر برگی بر درختان به حرکت در نیاید و دریا صاف و بی‌حرکت بماند.
2 Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
سپس، فرشتهٔ دیگری را دیدم که از مشرق می‌آمد و مهر بزرگ خدای زنده را به همراه می‌آورد. او به آن چهار فرشته‌ای که قدرت داشتند به زمین و دریا صدمه بزنند، گفت:
3 “Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
«دست نگه دارید! به دریا و زمین و درختان آسیبی نرسانید، تا مهر خدا را به پیشانی بندگان او بزنم.»
4 Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
تعداد کسانی که از تمام قبیله‌های بنی‌اسرائیل مهر شدند، یکصد و چهل و چهار هزار نفر بود، از هر قبیله دوازده هزار. اسامی قبیله‌ها عبارت بودند از: یهودا، رئوبین، جاد، اشیر، نفتالی، منسی، شمعون، لاوی، یساکار، زبولون، یوسف و بنیامین.
5 Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
6 daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
7 daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
8 daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
9 Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
پس از آن، دیدم که گروه بزرگی از تمام قومها، قبیله‌ها، نژادها و زبانها، در پیشگاه تخت و در برابر برّه ایستاده‌اند. تعداد ایشان چنان زیاد بود که امکان شمارش وجود نداشت. ایشان لباسی سفید بر تن داشتند و در دستشان شاخه‌های نخل دیده می‌شد.
10 Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
آنان همگی با صدای بلند می‌گفتند: «نجات ما از جانب خدای ما که بر تخت نشسته، و از جانب برّه است.»
11 Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
در این هنگام، تمام فرشتگان گرداگرد تخت و پیران و چهار موجود زنده ایستادند. سپس، آنان در مقابل تخت سجده کرده، خدا را پرستش نمودند،
12 suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn g165)
و گفتند: «آمین! حمد و جلال و حکمت، سپاس و حرمت، قدرت و قوت از آن خدای ما باد، تا به ابد. آمین!» (aiōn g165)
13 Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
آنگاه یکی از آن بیست و چهار پیر به من رو کرد و پرسید: «آیا می‌دانی این سفیدپوشان چه کسانی هستند و از کجا آمده‌اند؟»
14 Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
جواب دادم: «این را تو می‌دانی، سرورم.» به من گفت: «اینها همان کسانی هستند که از عذاب سخت بیرون آمده‌اند. ایشان لباسهای خود را با خون”برّه“شسته و سفید کرده‌اند.
15 Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
به همین جهت، اکنون در حضور تخت خدا هستند و او را شبانه روز در معبد او خدمت می‌کنند. او که بر تخت نشسته است، ایشان را در حضور خود پناه می‌دهد.
16 ‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
آنان از این پس، از گرسنگی و تشنگی و گرمای سوزان نیمروز در امان خواهند بود،
17 Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”
زیرا”برّه“که پیش تخت ایستاده است، ایشان را خوراک داده، شبان آنان خواهد بود و ایشان را به چشمه‌های آب حیات هدایت خواهد کرد؛ و خدا هر اشکی را از چشمان ایشان پاک خواهد نمود.»

< Ru’uya ta Yohanna 7 >