< Ru’uya ta Yohanna 7 >

1 Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
Pärast seda ma nägin nelja inglit seismas maailma neljas otsas, hoidmas kinni maailma nelja tuult, et tuul ei puhuks maa ega mere ega ühegi puu peale.
2 Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
Ja ma nägin, et idakaarest tõusis veel üks ingel, ja tal oli käes elava Jumala pitsat. Ta hüüdis valju häälega nelja ingli poole, kellele oli antud võim kahjustada maad ja merd:
3 “Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
„Ärge tehke kahju maale, merele ega puudele, enne kui me oleme pannud pitseri oma Jumala sulaste otsaesisele!“
4 Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
Ma kuulsin pitseriga märgitute arvu – sada nelikümmend neli tuhat kõigist Iisraeli suguharudest:
5 Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
Juuda suguharust märgiti pitseriga kaksteist tuhat, Ruubeni suguharust kaksteist tuhat, Gaadi suguharust kaksteist tuhat,
6 daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
Aaseri suguharust kaksteist tuhat, Naftali suguharust kaksteist tuhat, Manasse suguharust kaksteist tuhat,
7 daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
Siimeoni suguharust kaksteist tuhat, Leevi suguharust kaksteist tuhat, Issakari suguharust kaksteist tuhat,
8 daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
Sebuloni suguharust kaksteist tuhat, Joosepi suguharust kaksteist tuhat, Benjamini suguharust kaksteist tuhat pitseriga märgitut.
9 Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
Pärast seda ma vaatasin: ennäe, suur rahvahulk, keda keegi ei suutnud kokku lugeda, igast hõimust, suguharust, rahvast ja keelest. Need seisid trooni ja Talle ees, valged rüüd seljas ja palmioksad käes.
10 Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
Nad hüüdsid valju häälega: „Pääste on meie Jumalal, kes istub troonil, ja Tallel!“
11 Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
Ja kõik inglid, kes seisid trooni, vanemate ja nelja olevuse ümber, heitsid trooni ette silmili maha ja kummardasid Jumalat.
12 suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn g165)
Nad hüüdsid: „Aamen! Kiitus ja austus ja tarkus ja tänu ja au ja vägi ja tugevus olgu meie Jumalale igavesest ajast igavesti! Aamen.“ (aiōn g165)
13 Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
Siis pöördus üks vanemaist minu poole küsimusega: „Kes on need valgetes rüüdes ja kust nad tulevad?“
14 Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
Ma vastasin: „Mu isand, sina tead seda!“Ja ta ütles mulle: „Nemad on need, kes tulevad suure viletsuse keskelt. Nad on puhtaks pesnud oma rüüd ja teinud need valgeks Talle veres.
15 Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
Seepärast nad on Jumala trooni ees ja teenivad teda ööd ja päevad tema templis, ja see, kes istub troonil, varjab neid oma kohalolekuga.
16 ‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
„Neile ei tule iial enam nälga ega iial enam janu, ka ei põleta neid päike“ega palavus.
17 Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”
Sest Tall, kes on trooni keskel, hoiab neid kui karjane, „ta juhatab nad eluvee allikaile“. „Ja Jumal pühib ära kõik pisarad nende silmist.““

< Ru’uya ta Yohanna 7 >