< Ru’uya ta Yohanna 7 >

1 Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace.
And after this I saw four angels standing on the four corners of the earth, holding the four winds of the earth, that the wind might not blow on the earth, nor on the sea, nor on any tree.
2 Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce,
And I saw another angel ascending from the east, having the seal of the living God: and he cried with a loud voice to the four angels, to whom it was given to hurt the earth and the sea,
3 “Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.”
saying: Hurt not the earth, nor the sea, nor the trees, till we have sealed the servants of our God on their foreheads.
4 Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.
And I heard the number of those who were sealed: a hundred and forty-four thousand were sealed out of all the tribes of the sons of Israel.
5 Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin, daga kabilar Ruben mutum 12,000, daga kabilar Gad mutum 12,000,
Of the tribe of Judah, twelve thousand were sealed: of the tribe of Reuben, twelve thousand were sealed: of the tribe of Gad, twelve thousand were sealed:
6 daga kabilar Asher mutum 12,000, daga kabilar Naftali mutum 12,000, daga kabilar Manasse mutum 12,000,
of the tribe of Asher, twelve thousand were sealed: of the tribe of Naphtali, twelve thousand were sealed: of the tribe of Manasseh, twelve thousand were sealed:
7 daga kabilar Simeyon mutum 12,000, daga kabilar Lawi mutum 12,000, daga kabilar Issakar mutum 12,000,
of the tribe of Simeon, twelve thousand were sealed: of the tribe of Levi, twelve thousand were sealed: of the tribe of Issachar, twelve thousand were sealed:
8 daga kabilar Zebulun mutum 12,000, daga kabilar Yusuf mutum 12,000, daga kabilar Benyamin mutum 12,000.
of the tribe of Zabulon, twelve thousand were sealed: of the tribe of Joseph, twelve thousand were sealed: of the tribe of Benjamin, twelve thousand were sealed.
9 Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu.
After this I saw, and behold, a great multitude, that no one could number, out of all nations and tribes and peoples and tongues, standing before the throne, and before the Lamb, clothed with white robes, and there were palms in their hands;
10 Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa, “Ceto na Allahnmu ne, wanda yake zaune a bisan kursiyi, da kuma na Ɗan Ragon.”
and they cried with a loud voice, saying: Salvation to our God, who sits on the throne, and to the Lamb.
11 Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada,
And all the angels stood round about the throne and the elders and the four living creatures; and they fell on their faces before the throne, and worshiped God,
12 suna cewa, “Amin! Yabo da ɗaukaka, da hikima da godiya da girma da iko da ƙarfi sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin. Amin!” (aiōn g165)
saying, Amen: blessing and glory and wisdom and thanks and honor and power and strength be to our God from acre to acre. Amen. (aiōn g165)
13 Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”
And one of the elders answered, and said to me: Who are these that are clothed in white robes, and whence came they?
14 Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.” Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan.
And I said to him: Sir, thou knowest. And he said to me: These are they who have come out of great affliction, and have washed their robes, and made them white in the blood of the Lamb.
15 Saboda haka, “suna a gaban kursiyin Allah suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa; kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.
Therefore, they are before the throne of God, and serve him day and night in his temple; and he that sits on the throne shall dwell among them.
16 ‘Ba za su sāke jin yunwa ba; ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba. Rana ba za tă buga su ba,’ ko kuma kowane irin zafin ƙuna.
They shall hunger no more, nor shall they thirst any more, nor shall the sun fall upon them, nor any heat.
17 Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu; ‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’ ‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’”
For the Lamb that is in the midst of the throne will be their shepherd, and will lead them to living fountains of water: and God will wipe away every tear from their eyes.

< Ru’uya ta Yohanna 7 >