< Ru’uya ta Yohanna 6 >

1 Na kalli yayinda Ɗan Ragon ya buɗe hatimin farko na hatimai bakwai ɗin nan. Sai na ji ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai ya yi magana da murya mai kama da tsawa ya ce, “Zo!”
Je vis que l'agneau ouvrait l'un des sept sceaux, et j'entendis l'un des quatre êtres vivants qui disait, comme d'une voix de tonnerre: « Viens et vois! »
2 Na duba, can kuwa a gabana ga wani farin doki! Mai hawansa yana riƙe da baka, aka kuma ba shi rawani, ya yi sukuwa ya fito kamar mai nasara da ya kutsa don nasara.
Alors apparut un cheval blanc, et celui qui le montait tenait un arc. Une couronne lui fut donnée, et il sortit en vainqueur, et pour vaincre.
3 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na biyun, sai na ji halitta mai rai na biyu ya ce, “Zo!”
Quand il ouvrit le second sceau, j'entendis le second être vivant qui disait: « Viens! »
4 Sai wani doki ya fito, ja wur. Aka ba wa mai hawansa iko yă ɗauke salama daga duniya yă kuma sa mutane su kashe juna. Aka ba shi babban takobi.
Un autre sortit, un cheval roux. A celui qui le montait fut donné le pouvoir d'enlever la paix de la terre, et de faire en sorte que les hommes s'entretuent. Une grande épée lui fut donnée.
5 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na uku, sai na ji halitta mai rai na uku ya ce, “Zo!” Na duba, can a gabana kuwa ga wani baƙin doki! Mai hawansa yana riƙe da abubuwan awo guda biyu a hannunsa.
Quand il ouvrit le troisième sceau, j'entendis le troisième être vivant qui disait: « Viens et vois! » Et voici, il y avait un cheval noir, et celui qui le montait tenait une balance dans sa main.
6 Sai na ji wani abu mai ƙara kamar wata murya a tsakiyar halittu huɗun nan masu rai tana cewa, “Kwatan alkama don albashin aikin yini, da kuma kwata uku na sha’ir don albashin yini guda, kada kuwa ka ɓata man da ruwan inabi!”
J'entendis une voix au milieu des quatre êtres vivants qui disait: « Un chœnix de blé pour un denier, et trois chœnix d'orge pour un denier! N'abîmez pas l'huile et le vin! »
7 Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na huɗu, sai na ji muryar halitta mai rai na huɗu ya ce, “Zo!”
Quand il ouvrit le quatrième sceau, j'entendis le quatrième être vivant qui disait: « Viens et vois! »
8 Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya. (Hadēs g86)
Et voici, il y avait un cheval pâle, et le nom de celui qui le montait était la mort. L'Hadès le suivait. Il lui fut donné autorité sur le quart de la terre, pour tuer par l'épée, par la famine, par la mort, et par les bêtes sauvages de la terre. (Hadēs g86)
9 Sa’ad da ya buɗe hatimi na biyar, sai na ga a ƙarƙashin bagaden rayukan waɗanda aka kashe saboda maganar Allah da kuma shaidar da suka yi.
Quand il ouvrit le cinquième sceau, je vis sous l'autel les âmes de ceux qui avaient été tués à cause de la Parole de Dieu et du témoignage de l'Agneau qu'ils avaient.
10 Suka yi kira da babbar murya suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarki da kuma Mai Gaskiya, sai yaushe za ka shari’anta mazaunan duniya ka kuma ɗauki mana fansar jininmu?”
Ils criaient d'une voix forte, en disant: « Jusques à quand, Maître, le saint et le vrai, jugeras-tu et vengeras-tu notre sang sur les habitants de la terre? »
11 Sai aka ba wa kowannensu farin riga, aka kuma faɗa musu su ɗan jira kaɗan sai an cika adadin abokansu masu hidima da kuma’yan’uwansu waɗanda za a kashe kamar yadda su ma aka kashe su.
On donna à chacun d'eux une longue robe blanche. On leur dit qu'ils devaient se reposer encore quelque temps, jusqu'à ce que leurs compagnons de service et leurs frères, qui seraient aussi tués comme eux, aient achevé leur course.
12 Ina kallo yayinda ya buɗe hatimi na shida. Sai aka yi babban girgizar ƙasa. Rana ta zama baƙa kamar gwado na gashin akuya, wata kuma gaba ɗaya ya zama ja wur kamar jini,
Je vis, quand il ouvrit le sixième sceau, qu'il y eut un grand tremblement de terre. Le soleil devint noir comme un sac de crin, et la lune entière devint comme du sang.
13 taurarin sararin sama suka fāffāɗi a ƙasa, kamar yadda ɗanyun’ya’yan ɓaure suke fāɗuwa daga itacen ɓaure sa’ad da iska mai ƙarfi ta jijjiga shi.
Les étoiles du ciel tombèrent sur la terre, comme un figuier qui laisse tomber ses figues non mûres quand il est secoué par un grand vent.
14 Sararin sama kuwa ya janye kamar naɗaɗɗen littafi, ya yi ta naɗewa, aka kuma kawar da kowane dutse da kowane tsibiri daga wurinsa.
Le ciel fut enlevé comme un rouleau qu'on enroule. Toute montagne et toute île furent déplacées de leur place.
15 Sa’an nan sarakunan duniya, hakimai, jarumawa, masu arziki, masu ƙarfi, da kowane bawa da kuma kowane’yantacce ya ɓoye a cikin koguna da kuma cikin duwatsun tsaunuka.
Les rois de la terre, les princes, les chefs militaires, les riches, les forts, tous les esclaves et les hommes libres, se cachèrent dans les cavernes et dans les rochers des montagnes.
16 Suka kira duwatsu da tsaunuka suna cewa, “Ku fāɗi a kanmu ku kuma ɓoye mu daga fuskar wannan mai zama a kan kursiyi da kuma daga fushin Ɗan Ragon nan!
Et ils disaient aux montagnes et aux rochers: « Tombez sur nous, et cachez-nous devant la face de celui qui est assis sur le trône, et devant la colère de l'agneau,
17 Gama babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya tsayawa?”
car le grand jour de sa colère est venu, et qui peut subsister? ».

< Ru’uya ta Yohanna 6 >