< Ru’uya ta Yohanna 4 >

1 Bayan wannan sai na duba, a can kuma a gabana ga ƙofa a buɗe a sama. Sai muryar da na ji da fari da take magana da ni mai kama da busar ƙaho ta ce, “Hauro nan, zan kuma nuna maka abin da lalle zai faru bayan wannan.”
Depois destas coisas olhei e vi uma porta aberta no céu; e a primeira voz que ouvi, como uma trombeta falando comigo, foi uma que dizia: “Suba aqui, e eu lhe mostrarei as coisas que devem acontecer depois disto”.
2 Nan da nan sai ga ni cikin Ruhu, a can a gabana kuwa ga kursiyi a cikin sama da wani zaune a kansa.
Imediatamente eu estava no Espírito. Eis que havia um trono colocado no céu, e um sentado no trono
3 Wannan mai zama a can kuwa yana da kamannin dutsen yasfa da karneliya. Bakan gizo, mai kama da zumurrudu, ya kewaye kursiyin.
that parecia uma pedra de jaspe e um sárdio. Havia um arco-íris ao redor do trono, como uma esmeralda para se olhar.
4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyoyi ashirin da huɗu, zaune a kansu kuwa dattawa ashirin da huɗu ne. Suna saye da fararen tufafi suna kuma da rawanin zinariya a kawunansu.
Ao redor do trono havia vinte e quatro tronos. Nos tronos havia vinte e quatro anciãos sentados, vestidos com roupas brancas, com coroas de ouro em suas cabeças.
5 Daga kursiyin hasken walƙiya yana ta fitowa, da ƙararraki da kuma tsawa. A gaban kursiyin, fitilu bakwai suna ci. Waɗannan ne ruhohi bakwai na Allah.
Fora do trono prosseguiam relâmpagos, sons e trovões. Antes de seu trono, havia sete lâmpadas de fogo acesas, que são os sete Espíritos de Deus.
6 Haka kuma a gaban kursiyin akwai wani abu mai kama da tekun gilashi, yana ƙyalli kamar madubi. A tsakiya kuwa, kewaye da kursiyin, akwai halittu huɗu masu rai, cike kuma suna da idanu gaba da baya.
Antes do trono havia algo como um mar de vidro, semelhante ao cristal. No meio do trono, e ao redor do trono, havia quatro seres vivos cheios de olhos antes e depois.
7 Halitta ta fari tana kama da zaki, ta biyun kuwa tana kama da bijimi, ta ukun kuma tana da fuska kamar ta mutum, ta huɗun kuma tana kama da gaggafa mai tashi sama.
A primeira criatura era como um leão, a segunda como um bezerro, a terceira tinha um rosto como um homem, e a quarta era como uma águia voadora.
8 Kowace a cikin halittu huɗu masu rai ɗin nan tana da fikafikai guda shida, tana kuma cike da idanu a ko’ina, har ma ƙarƙashin fikafikanta. Dare da rana ba sa fasa cewa,
As quatro criaturas vivas, cada uma delas com seis asas, estão cheias de olhos ao redor e dentro. Eles não têm descanso dia e noite, dizendo: “Santo, santo, santo é o Senhor Deus, o Todo-Poderoso, quem foi e quem é e quem virá”!
9 Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn g165)
Quando os seres vivos dão glória, honra e graças àquele que está sentado no trono, àquele que vive para todo o sempre, (aiōn g165)
10 sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn g165)
os vinte e quatro anciãos caem diante daquele que está sentado no trono e adoram aquele que vive para todo o sempre, e lançam suas coroas diante do trono, dizendo: (aiōn g165)
11 “Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”
“Digno és tu, nosso Senhor e Deus, o Santo, de receber a glória, a honra e o poder, pois tu criaste todas as coisas, e por teu desejo elas existiram e foram criadas”!

< Ru’uya ta Yohanna 4 >