< Ru’uya ta Yohanna 4 >

1 Bayan wannan sai na duba, a can kuma a gabana ga ƙofa a buɗe a sama. Sai muryar da na ji da fari da take magana da ni mai kama da busar ƙaho ta ce, “Hauro nan, zan kuma nuna maka abin da lalle zai faru bayan wannan.”
Après cela je vis, et voici, une porte était ouverte dans le ciel, et la première voix que j'avais entendue, comme d'une trompette qui me parlait, disait: « Monte ici, et je te montrerai tout ce qui doit arriver après cela. »
2 Nan da nan sai ga ni cikin Ruhu, a can a gabana kuwa ga kursiyi a cikin sama da wani zaune a kansa.
Aussitôt je me trouvai inspiré; et voici, un trône était dressé dans le ciel, et sur ce trône Quelqu'un était assis.
3 Wannan mai zama a can kuwa yana da kamannin dutsen yasfa da karneliya. Bakan gizo, mai kama da zumurrudu, ya kewaye kursiyin.
Et Celui qui était assis était semblable par Son aspect à une pierre de jaspe et de cornaline, et il y avait autour du trône un arc-en-ciel semblable par son aspect à une émeraude.
4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyoyi ashirin da huɗu, zaune a kansu kuwa dattawa ashirin da huɗu ne. Suna saye da fararen tufafi suna kuma da rawanin zinariya a kawunansu.
Et autour du trône je vis vingt-quatre trônes, et sur les vingt-quatre trônes des anciens assis, revêtus de vêtements blancs, et sur leurs têtes des couronnes d'or.
5 Daga kursiyin hasken walƙiya yana ta fitowa, da ƙararraki da kuma tsawa. A gaban kursiyin, fitilu bakwai suna ci. Waɗannan ne ruhohi bakwai na Allah.
Et du trône sortent des éclairs, et des voix, et des tonnerres; et sept lampes de feu brûlent devant le trône, qui sont les sept esprits de Dieu.
6 Haka kuma a gaban kursiyin akwai wani abu mai kama da tekun gilashi, yana ƙyalli kamar madubi. A tsakiya kuwa, kewaye da kursiyin, akwai halittu huɗu masu rai, cike kuma suna da idanu gaba da baya.
Et devant le trône il y a comme une mer vitreuse semblable à du cristal; et au milieu du trône et autour du trône il y a quatre animaux pleins d'yeux par devant et par derrière.
7 Halitta ta fari tana kama da zaki, ta biyun kuwa tana kama da bijimi, ta ukun kuma tana da fuska kamar ta mutum, ta huɗun kuma tana kama da gaggafa mai tashi sama.
Et le premier animal est semblable à un lion, et le second animal est semblable à un veau, et le troisième animal a le visage comme d'un homme, et le quatrième animal est semblable à un aigle qui vole.
8 Kowace a cikin halittu huɗu masu rai ɗin nan tana da fikafikai guda shida, tana kuma cike da idanu a ko’ina, har ma ƙarƙashin fikafikanta. Dare da rana ba sa fasa cewa,
Et les quatre animaux, chacun d'eux ayant six ailes, sont remplis d'yeux tout autour et intérieurement; et ils ne cessent jour et nuit de dire: « Saint, saint, saint, le Seigneur Dieu, Le Tout-Puissant, Qui était et qui est et qui doit venir! »
9 Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn g165)
Et tant que les animaux rendront gloire, honneur et actions de grâces à Celui qui est assis sur le trône, à Celui qui vit aux siècles des siècles, (aiōn g165)
10 sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn g165)
les vingt-quatre anciens se prosterneront devant Celui qui est assis sur le trône et adoreront Celui qui vit aux siècles des siècles, et jetteront leurs couronnes devant le trône en disant: (aiōn g165)
11 “Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”
« Tu es digne, notre Seigneur et notre Dieu, De recevoir la gloire, et l'honneur, et la puissance; Car Tu as créé toutes choses, Et c'est par Ta volonté qu'elles ont eu l'être. »

< Ru’uya ta Yohanna 4 >