< Ru’uya ta Yohanna 4 >

1 Bayan wannan sai na duba, a can kuma a gabana ga ƙofa a buɗe a sama. Sai muryar da na ji da fari da take magana da ni mai kama da busar ƙaho ta ce, “Hauro nan, zan kuma nuna maka abin da lalle zai faru bayan wannan.”
Après cela je regardai, et voici une porte était ouverte dans le ciel; et la première voix que j'avais entendue, comme celle d'une trompette, et qui parlait avec moi, dit: Monte ici, et je te ferai voir les choses qui doivent arriver après celles-ci.
2 Nan da nan sai ga ni cikin Ruhu, a can a gabana kuwa ga kursiyi a cikin sama da wani zaune a kansa.
Et aussitôt je fus ravi en esprit; et voici, un trône était dressé dans le ciel, et quelqu'un était assis sur ce trône.
3 Wannan mai zama a can kuwa yana da kamannin dutsen yasfa da karneliya. Bakan gizo, mai kama da zumurrudu, ya kewaye kursiyin.
Et celui qui était assis, paraissait semblable à une pierre de jaspe et de sardoine; et le trône était entouré d'un arc-en-ciel, qui paraissait comme une émeraude.
4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyoyi ashirin da huɗu, zaune a kansu kuwa dattawa ashirin da huɗu ne. Suna saye da fararen tufafi suna kuma da rawanin zinariya a kawunansu.
Autour du trône il y avait vingt-quatre autres trônes; et je vis sur ces trônes vingt-quatre Anciens assis, vêtus de vêtements blancs, et ayant sur leurs têtes des couronnes d'or.
5 Daga kursiyin hasken walƙiya yana ta fitowa, da ƙararraki da kuma tsawa. A gaban kursiyin, fitilu bakwai suna ci. Waɗannan ne ruhohi bakwai na Allah.
Et du trône sortaient des éclairs, des tonnerres et des voix; et devant le trône brûlaient sept lampes ardentes, qui sont les sept esprits de Dieu.
6 Haka kuma a gaban kursiyin akwai wani abu mai kama da tekun gilashi, yana ƙyalli kamar madubi. A tsakiya kuwa, kewaye da kursiyin, akwai halittu huɗu masu rai, cike kuma suna da idanu gaba da baya.
Il y avait aussi devant le trône une mer de verre semblable à du cristal, et au milieu du trône et autour du trône, quatre animaux pleins d'yeux devant et derrière.
7 Halitta ta fari tana kama da zaki, ta biyun kuwa tana kama da bijimi, ta ukun kuma tana da fuska kamar ta mutum, ta huɗun kuma tana kama da gaggafa mai tashi sama.
Le premier animal ressemblait à un lion; le second animal ressemblait à un veau; le troisième animal avait le visage comme un homme; et le quatrième animal ressemblait à un aigle qui vole.
8 Kowace a cikin halittu huɗu masu rai ɗin nan tana da fikafikai guda shida, tana kuma cike da idanu a ko’ina, har ma ƙarƙashin fikafikanta. Dare da rana ba sa fasa cewa,
Et les quatre animaux avaient chacun six ailes, et à l'entour et au-dedans ils étaient pleins d'yeux; et ils ne cessaient, jour et nuit, de dire: Saint, saint, saint est le Seigneur Dieu tout-puissant, QUI ÉTAIT, QUI EST, et QUI SERA!
9 Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn g165)
Et quand les animaux rendaient gloire et honneur et grâce à celui qui était assis sur le trône, à celui qui vit aux siècles des siècles, (aiōn g165)
10 sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn g165)
Les vingt-quatre Anciens se prosternaient devant celui qui était assis sur le trône, et ils adoraient celui qui vit aux siècles des siècles et jetaient leurs couronnes devant le trône, en disant: (aiōn g165)
11 “Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”
Seigneur, tu es digne de recevoir la gloire, l'honneur, et la puissance; car tu as créé toutes choses, et c'est par ta volonté qu'elles existent, et ont été créées.

< Ru’uya ta Yohanna 4 >