< Ru’uya ta Yohanna 4 >
1 Bayan wannan sai na duba, a can kuma a gabana ga ƙofa a buɗe a sama. Sai muryar da na ji da fari da take magana da ni mai kama da busar ƙaho ta ce, “Hauro nan, zan kuma nuna maka abin da lalle zai faru bayan wannan.”
After these things I saw, and behold, a door opened in heaven, and the first voice which I heard, [a voice] as of a trumpet speaking with me, one saying, Come up hither, and I will shew thee the things which must come to pass hereafter.
2 Nan da nan sai ga ni cikin Ruhu, a can a gabana kuwa ga kursiyi a cikin sama da wani zaune a kansa.
Straightway I was in the Spirit: and behold, there was a throne set in heaven, and one sitting upon the throne;
3 Wannan mai zama a can kuwa yana da kamannin dutsen yasfa da karneliya. Bakan gizo, mai kama da zumurrudu, ya kewaye kursiyin.
and he that sat [was] to look upon like a jasper stone and a sardius: and [there was] a rainbow round about the throne, like an emerald to look upon.
4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyoyi ashirin da huɗu, zaune a kansu kuwa dattawa ashirin da huɗu ne. Suna saye da fararen tufafi suna kuma da rawanin zinariya a kawunansu.
And round about the throne [were] four and twenty thrones: and upon the thrones [I saw] four and twenty elders sitting, arrayed in white garments; and on their heads crowns of gold.
5 Daga kursiyin hasken walƙiya yana ta fitowa, da ƙararraki da kuma tsawa. A gaban kursiyin, fitilu bakwai suna ci. Waɗannan ne ruhohi bakwai na Allah.
And out of the throne proceed lightnings and voices and thunders. And [there were] seven lamps of fire burning before the throne, which are the seven Spirits of God;
6 Haka kuma a gaban kursiyin akwai wani abu mai kama da tekun gilashi, yana ƙyalli kamar madubi. A tsakiya kuwa, kewaye da kursiyin, akwai halittu huɗu masu rai, cike kuma suna da idanu gaba da baya.
and before the throne, as it were a glassy sea like unto crystal; and in the midst of the throne, and round about the throne, four living creatures full of eyes before and behind.
7 Halitta ta fari tana kama da zaki, ta biyun kuwa tana kama da bijimi, ta ukun kuma tana da fuska kamar ta mutum, ta huɗun kuma tana kama da gaggafa mai tashi sama.
And the first creature [was] like a lion, and the second creature like a calf, and the third creature had a face as of a man, and the fourth creature [was] like a flying eagle.
8 Kowace a cikin halittu huɗu masu rai ɗin nan tana da fikafikai guda shida, tana kuma cike da idanu a ko’ina, har ma ƙarƙashin fikafikanta. Dare da rana ba sa fasa cewa,
And the four living creatures, having each one of them six wings, are full of eyes round about and within: and they have no rest day and night, saying, Holy, holy, holy, [is] the Lord God, the Almighty, which was and which is and which is to come.
9 Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn )
And when the living creatures shall give glory and honour and thanks to him that sitteth on the throne, to him that liveth for ever and ever, (aiōn )
10 sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn )
the four and twenty elders shall fall down before him that sitteth on the throne, and shall worship him that liveth for ever and ever, and shall cast their crowns before the throne, saying, (aiōn )
11 “Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”
Worthy art thou, our Lord and our God, to receive the glory and the honour and the power: for thou didst create all things, and because of thy will they were, and were created.