< Ru’uya ta Yohanna 4 >

1 Bayan wannan sai na duba, a can kuma a gabana ga ƙofa a buɗe a sama. Sai muryar da na ji da fari da take magana da ni mai kama da busar ƙaho ta ce, “Hauro nan, zan kuma nuna maka abin da lalle zai faru bayan wannan.”
ܡܢ ܒܬܪ ܗܠܝܢ ܚܙܝܬ ܘܗܐ ܬܪܥܐ ܦܬܝܚܐ ܒܫܡܝܐ ܘܩܠܐ ܗܘ ܕܫܡܥܬ ܐܝܟ ܫܝܦܘܪܐ ܡܠܠ ܥܡܝ ܠܡܐܡܪ ܤܩ ܠܗܪܟܐ ܘܐܚܘܝܟ ܡܐ ܕܝܗܝܒ ܠܡܗܘܐ ܒܬܪ ܗܠܝܢ
2 Nan da nan sai ga ni cikin Ruhu, a can a gabana kuwa ga kursiyi a cikin sama da wani zaune a kansa.
ܘܡܚܕܐ ܗܘܝܬ ܒܪܘܚ ܘܗܐ ܟܘܪܤܝܐ ܤܝܡ ܒܫܡܝܐ ܘܥܠ ܟܘܪܤܝܐ ܝܬܒ
3 Wannan mai zama a can kuwa yana da kamannin dutsen yasfa da karneliya. Bakan gizo, mai kama da zumurrudu, ya kewaye kursiyin.
ܘܕܝܬܒ ܐܝܟ ܕܡܘܬܐ ܕܚܙܘܐ ܕܟܐܦܐ ܕܝܫܦܗ ܘܕܤܪܕܘܢ ܘܩܫܬܐ ܕܥܢܢܐ ܕܚܕܪܘܗܝ ܕܟܘܪܤܝܐ ܕܡܘܬ ܚܙܘܐ ܕܙܡܪܓܕܐ
4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyoyi ashirin da huɗu, zaune a kansu kuwa dattawa ashirin da huɗu ne. Suna saye da fararen tufafi suna kuma da rawanin zinariya a kawunansu.
ܘܚܕܪ ܟܘܪܤܝܐ ܟܘܪܤܘܬܐ ܥܤܪܝܢ ܘܐܪܒܥܐ ܘܥܠܝܗܘܢ ܕܝܢ ܕܟܘܪܤܘܬܐ ܥܤܪܝܢ ܘܐܪܒܥܐ ܩܫܝܫܝܢ ܕܝܬܒܝܢ ܕܥܛܝܦܝܢ ܡܐܢܐ ܚܘܪܐ ܘܥܠ ܩܪܩܦܬܗܘܢ ܟܠܝܠܐ ܕܕܗܒܐ
5 Daga kursiyin hasken walƙiya yana ta fitowa, da ƙararraki da kuma tsawa. A gaban kursiyin, fitilu bakwai suna ci. Waɗannan ne ruhohi bakwai na Allah.
ܘܡܢ ܟܘܪܤܘܬܐ ܢܦܩܝܢ ܪܥܡܐ ܘܒܪܩܐ ܘܩܠܐ ܘܫܒܥܐ ܢܗܝܪܐ ܕܝܩܕܝܢ ܩܕܡܘܗܝ ܕܟܘܪܤܝܐ ܐܝܠܝܢ ܕܐܝܬܝܗܘܢ ܫܒܥ ܪܘܚܝܢ ܕܐܠܗܐ
6 Haka kuma a gaban kursiyin akwai wani abu mai kama da tekun gilashi, yana ƙyalli kamar madubi. A tsakiya kuwa, kewaye da kursiyin, akwai halittu huɗu masu rai, cike kuma suna da idanu gaba da baya.
ܘܩܕܡ ܟܘܪܤܝܐ ܝܡܐ ܕܙܓܘܓܝܬܐ ܐܝܟ ܕܘܡܝܐ ܕܓܠܝܕܐ ܘܒܡܨܥܬ ܟܘܪܤܝܐ ܘܚܕܪܘܗܝ ܕܟܘܪܤܝܐ ܐܪܒܥ ܚܝܘܢ ܕܡܠܝܢ ܥܝܢܐ ܡܢ ܩܕܡܝܗܝܢ ܘܡܢ ܒܤܬܪܗܝܢ
7 Halitta ta fari tana kama da zaki, ta biyun kuwa tana kama da bijimi, ta ukun kuma tana da fuska kamar ta mutum, ta huɗun kuma tana kama da gaggafa mai tashi sama.
ܚܝܘܬܐ ܩܕܡܝܬܐ ܕܡܝܐ ܠܐܪܝܐ ܘܚܝܘܬܐ ܕܬܪܬܝܢ ܕܡܘܬܐ ܕܥܓܠܐ ܘܚܝܘܬܐ ܕܬܠܬ ܐܝܬ ܠܗ ܐܦܐ ܐܝܟ ܕܒܪܢܫܐ ܘܚܝܘܬܐ ܕܐܪܒܥ ܕܡܘܬܐ ܕܢܫܪܐ ܕܦܪܚ
8 Kowace a cikin halittu huɗu masu rai ɗin nan tana da fikafikai guda shida, tana kuma cike da idanu a ko’ina, har ma ƙarƙashin fikafikanta. Dare da rana ba sa fasa cewa,
ܐܪܒܥܬܝܗܝܢ ܚܝܘܬܐ ܟܠܚܕܐ ܡܢܗܝܢ ܩܝܡܐ ܘܐܝܬ ܠܗ ܡܢ ܛܦܪܝܗ ܘܠܥܠ ܫܬܐ ܓܦܝܢ ܚܘܕܪܢܐܝܬ ܘܡܢ ܠܓܘ ܡܠܝܢ ܥܝܢܐ ܘܫܠܝܐ ܠܝܬ ܠܗܝܢ ܐܝܡܡܐ ܘܠܠܝܐ ܠܡܐܡܪ ܩܕܝܫ ܩܕܝܫ ܩܕܝܫ ܡܪܝܐ ܐܠܗܐ ܐܚܝܕ ܟܠ ܗܘ ܕܐܝܬܘܗܝ ܗܘܐ ܘܐܝܬܘܗܝ ܘܐܬܐ
9 Duk lokacin da halittu masu ran nan suka rera ɗaukaka, girma da kuma godiya ga wannan wanda yake zaune a kan kursiyin da kuma wanda yake mai rai har abada abadin, (aiōn g165)
ܘܡܐ ܕܝܗܒ ܐܪܒܥܬܝܗܝܢ ܚܝܘܬܐ ܬܫܒܘܚܬܐ ܘܐܝܩܪܐ ܘܩܘܒܠ ܛܝܒܘܬܐ ܠܕܝܬܒ ܥܠ ܟܘܪܤܝܐ ܘܠܕܚܝ ܠܥܠܡ ܥܠܡܝܢ ܐܡܝܢ (aiōn g165)
10 sai dattawa ashirin da huɗun nan su fāɗi a ƙasa a gaban wannan wanda yake zaune a kursiyin, su yi sujada wa wannan wanda yake da rai har abada abadin. Sukan ajiye rawaninsu a gaban kursiyin suna cewa, (aiōn g165)
ܢܦܠܘܢ ܥܤܪܝܢ ܘܐܪܒܥܐ ܩܫܝܫܝܢ ܩܕܡ ܡܢ ܕܝܬܒ ܥܠ ܟܘܪܤܝܐ ܘܢܤܓܕܘܢ ܠܥܠܡ ܥܠܡܝܢ ܐܡܝܢ ܠܡܢ ܕܚܝ ܘܢܪܡܘܢ ܟܠܝܠܝܗܘܢ ܩܕܡ ܟܘܪܤܝܐ ܟܕ ܐܡܪܝܢ (aiōn g165)
11 “Ya Ubangijinmu da Allahnmu, ka cancanci ɗaukaka da girma da iko, domin ka halicci dukan abubuwa, kuma ta wurin nufinka aka halicce su suka kuma kasance.”
ܕܫܘܝܬ ܗܘ ܡܪܢ ܘܐܠܗܢ ܠܡܤܒ ܬܫܒܘܚܬܐ ܘܐܝܩܪܐ ܘܚܝܠܐ ܡܛܠ ܕܐܢܬ ܒܪܝܬ ܟܠ ܘܒܝܕ ܨܒܝܢܟ ܗܘܝ ܘܐܬܒܪܝ

< Ru’uya ta Yohanna 4 >