< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
In pokazal mi je čisto reko vode življenja, svetlo kakor kristal, izhajajočo iz prestola Božjega in jagnjetovega.
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
Sredi ulic njegovih in reke tam pa tam drevo življenja, ki dela sadov dvanajst, vsak mesec dajoč sad svoj; in listje drevesovo je v ozdravljenje narodov.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
In nobenega prokletstva ne bode več; in prestol Božji in jagnjetov bode v njem; in hlapci njegovi bodo mu služili;
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
In gledali bodo obličje njegovo, in ime njegovo na njih čelih.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
In noči ne bode tam; in potreba jim ni svetilnice in uči solnčne, ker Gospod Bog jih razsvetljuje; in kraljevali bodo na vekov veke. (aiōn )
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
In reče mi: Té besede so gotove in resnične; in Gospod, svetih prerokov Bog, poslal je angela svojega, kazat hlapcem svojim, kaj se ima zgoditi hitro.
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
Glej, hitro pridem. Blagor mu, kdor hrani besede prerokovanja té knjige!
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
In jaz Janez sem, ki sem videl to in slišal; in ko sem slišal in videl, padel sem molit pred noge angelove, kateri mi je to kazal.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
In reče mi: Nikar! kajti sohlapec sem tvoj in izmed bratov tvojih, prerokov, in njih, ki hranijo besede te knjige; Boga môli.
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
In reče mi: Ne zapečati besed prerokovanja te knjige; ker čas je blizu.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
Kdor dela krivico, naj jo dela še, in kdor je nesnažen bodi še nesnažen; in pravični opravičuj se še, in sveti naj se še posvečuje.
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
In glej, hitro pridem, in plačilo moje z menoj povrnit vsakemu, kakor bode delo njegovo.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
Jaz sem A in O, začetek in konec, prvi in zadnji.
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
Blagor jim, kateri delajo zapovedi njegove, da bode njih oblast do drevesa življenja, in skozi vrata vnidejo v mesto.
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
Zunaj pa psi in čarovniki in kurbirji in morilci in malikovalci, in vsak, kdor ljubi in dela laž.
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
Jaz Jezus poslal sem angela svojega, pričat vam to po občinah. Jaz sem korenina in rod Davidov, zvezda svetla in jutranja.
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
In Duh in nevesta govorita: Pridi! in kdor sliši, naj reče: Pridi! in kdor je žejen, pridi, in kdor hoče, vzemi vodo življenja zastonj!
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
Pričam namreč vsakemu, kdor sliši besede prerokovanja té knjige: Če temu kdo pridene, njega zadene Bog sè šibami, zapisanimi v tej knjigi.
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
In če kdo odvzame od besed knjige tega prerokovanja, odvzame mu Bog dél njegov od knjige življenja, in iz mesta svetega in kar je pisano v tej knjigi.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
On, ki to priča, govori: Dà, hitro pridem. Amen, dà, pridi, Gospod Jezus!
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
Milost Gospoda našega Jezusa Kristusa z vami vsemi! Amen.