< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
Wasengitshengisa umfula ocengekileyo wamanzi empilo, ukhazimula njengekristali, uphuma esihlalweni sobukhosi sikaNkulunkulu, leseWundlu.
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
Laphakathi kwesitalada sawo, njalo ngapha langapha komfula kwakulesihlahla sempilo, sithela izithelo ezilitshumi lambili, ileyo laleyo inyanga sithela isithelo saso; lamahlamvu esihlahla ngawokwelatshwa kwezizwe.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
Kakusayikuba khona lakanye isiqalekiso; kodwa isihlalo sobukhosi sikaNkulunkulu leseWundlu sizakuba kuwo; lenceku zakhe zizamkhonza,
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
zizabona ubuso bakhe; lebizo lakhe lizakuba semabunzini azo.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
Lobusuku kabuyikuba khona lapho, njalo kazisweli isibane lokukhanya kwelanga, ngoba iNkosi uNkulunkulu iyazikhanyisela; njalo zizabusa kuze kube nini lanini. (aiōn )
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
Wasesithi kimi: Lamazwi athembekile aqotho; njalo iNkosi, uNkulunkulu wabaprofethi abangcwele, ithumele ingilosi yayo ukutshengisa inceku zayo izinto okumele zenzeke ngokuphangisa.
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
Khangela, ngiyeza masinyane. Ubusisiwe owagcinayo amazwi esiprofetho salolugwalo.
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
Futhi mina Johane nginguye owazibonayo lezizinto lowazizwayo. Kuthe sengizizwile ngazibona, ngawela phansi ukukhonza phambi kwenyawo zengilosi eyangitshengisa lezizinto.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
Yasisithi kimi: Qaphela ungakwenzi; ngoba ngiyinceku kanye lawe, labazalwane bakho abaprofethi, lalabo abagcina amazwi alolugwalo; khonza uNkulunkulu.
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
Yasisithi kimi: Unganamathiseli ngophawu amazwi esiprofetho salolugwalo; ngoba isikhathi siseduze.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
Owenza okungalunganga kahlale esenza okungalunganga; longcolileyo ahlale engcolile; lolungileyo ahlale elungisisiwe; longcwele ahlale engcwelisiwe.
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
Khangela-ke, ngiyeza masinyane, lomvuzo wami ukimi, ukuvuza ngulowo lalowo njengokuzakuba ngumsebenzi wakhe.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
Mina nginguAlfa loOmega, isiqalo lesicino, owokuqala lowokucina.
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
Babusisiwe labo abenza imilayo yakhe, ukuze babe lelungelo esihlahleni sempilo, babe sebengena emzini ngamasango;
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
kodwa ngaphandle kukhona izinja labathakathi leziphingi lababulali labakhonza izithombe laye wonke othanda njalo esenza amanga.
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
Mina Jesu ngithume ingilosi yami ukufakaza lezizinto kini emabandleni. Mina ngiyimpande lenzalo kaDavida, indonsakusa ekhazimulayo.
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
UMoya-ke lomakoti bathi: Woza! Lozwayo kathi: Woza! Lowomileyo keze; lothandayo kathathe amanzi empilo ngesihle.
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
Ngoba ngiyafakaza kuye wonke ozwa amazwi esiprofetho salolugwalo: Uba umuntu esengeza kulezizinto, uNkulunkulu uzakwengezelela kuye izinhlupheko ezilotshwe kulolugwalo;
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
njalo uba umuntu esusa okwamazwi ogwalo lwalesisiprofetho, uNkulunkulu uzasusa isabelo sakhe egwalweni lwempilo, lemzini ongcwele, lezintweni ezilotshiweyo kulolugwalo.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
Ofakaza lezizinto uthi: Yebo, ngiyeza masinyane. Ameni. Yebo, woza, Nkosi Jesu!
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
Umusa weNkosi yethu uJesu Kristu kawube lani lonke. Ameni.