< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
Et l'ange me montra le fleuve d'eau de la vie, clair comme du cristal; il sortait du trône de Dieu et de l'agneau.
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
Au milieu de la rue de la ville et des deux côtés du fleuve, se trouvent des arbres de vie qui donnent douze récoltes, une récolte par mois, et dont les feuilles servent à la guérison des nations.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
Il n'y aura plus d'anathème. Le trône de Dieu et de l'agneau sera dans la ville; les serviteurs de Dieu le serviront,
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
ils verront sa face, son nom sera sur leurs fronts.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
Il n'y aura point de nuit, et ils n'auront besoin ni de lampe, ni de lumière, parce que le Seigneur Dieu les illuminera; et ils régneront aux siècles des siècles. (aiōn )
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
Et l’ange me dit: «Ces paroles sont sûres et véritables; et le Seigneur, le Dieu des esprits des prophètes, a envoyé son ange, pour montrer à ses serviteurs les événements qui doivent bientôt arriver.
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
«Voici, je viens bientôt. «Heureux celui qui garde les paroles de la prophétie de ce livre!»
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
C'est moi, Jean, qui ai entendu et vu ces choses, et, après les avoir entendues et vues, je tombai aux pieds de l'ange qui me les montrait, pour l'adorer.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
Mais il me dit: «Garde-toi de le faire; je suis ton compagnon de service, le compagnon de tes frères, les prophètes, et de ceux qui gardent les paroles de ce livre: adore Dieu.»
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
Et il me dit: «Ne tiens point secrètes les paroles de la prophétie de ce livre; le moment est proche.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
«Que l'injuste fasse encore le mal; que l'impur se souille encore; que le juste pratique encore la justice, et que le saint se sanctifie encore.
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
Voici, je viens bientôt, et la rétribution est avec moi: je rendrai à chacun selon ses oeuvres.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
Je suis l'alpha et l'oméga, le premier et le dernier, le commencement et la fin.»
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
Heureux ceux qui pratiquent ses commandements, afin d'avoir droit à l'arbre de vie, et d'entrer dans la ville par les portes!
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
Dehors, les chiens, les magiciens, les libertins, les meurtriers, les idolâtres, et quiconque aime le mensonge et s'y adonne!
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
«C'est moi, Jésus, qui ai envoyé mon ange, pour vous annoncer ces choses, à vous, églises. C'est moi qui suis le rejeton et le fils de David, l'étoile brillante du matin.»
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
Et l'Esprit et l'épouse disent: «Viens.» Que celui qui entend, dise aussi: «Viens.» Que celui qui a soif, vienne. Que celui qui désire l'eau de la vie, en prenne gratuitement.
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
Je déclare à quiconque entend les paroles de ce livre, que si quelqu'un y ajoute, Dieu le frappera des calamités qui sont décrites dans ce livre;
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
et que, si quelqu'un retranche des paroles de ce livre prophétique, Dieu lui retranchera sa part de l'arbre de vie et l’exclura de la ville sainte, qui sont décrits dans ce livre.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
Celui qui atteste ces choses, dit: «Oui, je viens bientôt.» — «Amen! Viens, Seigneur Jésus!
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
Que la grâce du Seigneur Jésus soit avec tous!