< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
He showed me a river of water of life, clear as crystal, proceeding out of the throne of God and of the Lamb,
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
in the middle of its street. On this side of the river and on that was the tree of life, bearing twelve kinds of fruits, yielding its fruit every month. The leaves of the tree were for the healing of the nations.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
There will be no curse any more. The throne of God and of the Lamb will be in it, and his servants serve him.
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
They will see his face, and his name will be on their foreheads.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
There will no longer be any night, and they have no need for the light of a lamp or the light of the sun, because the Lord God will shine on them. And they will reign forever and ever. (aiōn )
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
He said to me, "These words are faithful and true. The Lord God of the spirits of the prophets sent his angel to show to his servants the things which must happen soon."
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
"Look, I am coming quickly. Blessed is he who keeps the words of the prophecy of this book."
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
Now I, John, am the one who heard and saw these things. When I heard and saw, I fell down to worship before the feet of the angel who had shown me these things.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
He said to me, "See you do not do it. I am a fellow servant with you and with your brothers, the prophets, and with those who keep the words of this book. Worship God."
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
He said to me, "Do not seal up the words of the prophecy of this book, for the time is near.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
He who acts unjustly, let him act unjustly still. He who is filthy, let him be filthy still. He who is righteous, let him do righteousness still. He who is holy, let him be holy still."
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
"Look, I am coming quickly. My reward is with me, to repay to each person according to his work.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
I am the Alpha and the Omega, the First and the Last, the Beginning and the End.
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
Blessed are they who wash their robes, that they may have the right to the tree of life, and may enter in by the gates into the city.
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
Outside are the dogs, the sorcerers, the sexually immoral, the murderers, the idolaters, and everyone who loves and practices falsehood.
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
I, Jesus, have sent my angel to testify these things to you for the churches. I am the root and the offspring of David; the bright morning star."
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
The Spirit and the bride say, "Come." He who hears, let him say, "Come." He who is thirsty, let him come. He who desires, let him take the water of life freely.
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
I testify to everyone who hears the words of the prophecy of this book, if anyone adds to them, God will add to him the plagues which are written in this book.
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
If anyone takes away from the words of the book of this prophecy, God will take away his part from the tree of life, and out of the holy city, which are written in this book.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
He who testifies these things says, "Yes, I come quickly." Amen. Come, Lord Jesus.
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
The grace of the Lord Jesus be with all.