< Ru’uya ta Yohanna 22 +

1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
And he showed me a river of water of life, clear as crystal, issuing out of the throne of God, and of the Lamb.
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
In the midst of the broad street, and on each side of the river, was the tree of life, producing twelve kinds of fruit-- producing its fruit in every month: and the leaves of the tree are for the healing of the nations.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
And every curse shall cease. And the throne of God, and of the Lamb, shall be in it; and his servants shall serve him.
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
And they shall see his face: and his name shall be borne upon their foreheads.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn g165)
And there shall be no more night; and they have no need of a lamp, nor of the light of the sun; because the Lord God shall enlighten them: and they shall reign for ever and ever. (aiōn g165)
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
And he said to me, These words are faithful and true. And the Lord God of the holy prophets, has sent his holy angel to show his servants what must quickly be done.
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
Behold, I come quickly: blessed is he who keeps the words of the prophecy of this book.
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
And I, John, saw and heard these things, and when I heard and saw them, I fell down to worship before the feet of the angel who showed me these things.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
And he said to me, See you do it not: I am a fellow-servant with you, and of your brethren, the prophets, and of those who keep the words of this book: worship God.
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
And he said to me, Seal not up the words of the prophecy of this book; for the time is near.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
Let him that is unjust, be unjust still; and let him that is polluted, be polluted still; and let him that is righteous, be righteous still; and let him that is holy, be holy still.
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
Behold, I come quickly; and my reward is with me: I will recompense to every man according as his works shall be.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
I am the Alpha and the Omega--the Beginning and the End: the First and the Last.
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
(Happy are they who keep his commandments, that they may have the privilege to eat of the tree of life; and they shall enter by the gates into the city.
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
Without are the dogs, and the sorcerers, and the fornicators, and the murderers, and the idolaters, and every one who loves and invents a lie.)
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
I, Jesus, have sent my angel to testify these things to you, in the congregations. I am the Root and the Offspring of David; the bright and the Morning Star.
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
And the Spirit and the Bride say, Come: and let him that hears, say, Come: and let him that is thirsty, come: whoever will, let him take of the water of life freely.
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
And I testify of every one that hears the words of the prophecy of this book, If any man add to these things, God shall add to him the plagues which are written in this book:
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
and if any one take away from the words of the book of this prophecy, God will take away his part out of the book of life, and out of the holy city--the things which are written in this book.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
He who testifies these things, says, Surely, I come quickly. Amen. Even so, come, Lord Jesus.
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
May the favor of the Lord Jesus Christ be with all the saints!

< Ru’uya ta Yohanna 22 +