< Ru’uya ta Yohanna 22 +
1 Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon,
And he showed me a river of water of life, clear as crystal, proceeding from the throne of God and of the Lamb.
2 yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da’ya’ya goma sha biyu, yana ba da’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne.
In the midst of the street thereof, and on both sides of the river, was the tree of life, bearing twelve fruits, yielding its fruits every month, and the leaves of the tree were for the healing of the nations.
3 Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima.
And there shall be no curse any more; but the throne of God and of the Lamb shall be in it, and his servants shall serve him.
4 Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu.
And they shall see his face: and his name shall be on their foreheads.
5 Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin. (aiōn )
And night shall be no more: and they shall not need the light of the lamp, nor the light of the sun, because the Lord God shall enlighten them, and they shall reign for ever and ever. (aiōn )
6 Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
And he said to me: These words are most faithful and true. And the Lord God of the spirits of the prophets sent his angel to shew his servants the things which must be done shortly.
7 “Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
And, Behold I come quickly. Blessed is he that keepeth the words of the prophecy of this book.
8 Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada.
And I, John, who have heard and seen these things. And after I had heard and seen, I fell down to adore before the feet of the angel, who shewed me these things.
9 Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
And he said to me: See thou do it not: for I am thy fellow servant, and of thy brethren the prophets, and of them that keep the words of the prophecy of this book. Adore God.
10 Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa.
And he saith to me: Seal not the words of the prophecy of this book: for the time is at hand.
11 Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
He that hurteth, let him hurt still: and he that is filthy, let him be filthy still: and he that is just, let him be justified still: and he that is holy, let him be sanctified still.
12 “Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi.
Behold, I come quickly; and my reward is with me, to render to every man according to his works.
13 Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
I am Alpha and Omega, the first and the last, the beginning and the end.
14 “Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi.
Blessed are they that wash their robes in the blood of the Lamb: that they may have a right to the tree of life, and may enter in by the gates into the city.
15 Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
Without are dogs, and sorcerers, and unchaste, and murderers, and servers of idols, and every one that loveth and maketh a lie.
16 “Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
I Jesus have sent my angel, to testify to you these things in the churches. I am the root and stock of David, the bright and morning star.
17 Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
And the spirit and the bride say: Come. And he that heareth, let him say: Come. And he that thirsteth, let him come: and he that will, let him take the water of life, freely.
18 Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan.
For I testify to every one that heareth the words of the prophecy of this book: If any man shall add to these things, God shall add unto him the plagues written in this book.
19 Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
And if any man shall take away from the words of the book of this prophecy, God shall take away his part out of the book of life, and out of the holy city, and from these things that are written in this book.
20 Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.” Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
He that giveth testimony of these things, saith, Surely I come quickly: Amen. Come, Lord Jesus.
21 Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
The grace of our Lord Jesus Christ be with you all. Amen.