< Ru’uya ta Yohanna 20 >

1 Na kuma ga wani mala’ika yana saukowa daga sama, yana da mabuɗin Abis yana kuma riƙe da ƙaton sarƙa a hannunsa. (Abyssos g12)
سپس، فرشته‌ای را دیدم که از آسمان پایین آمد. او کلید چاه بی‌انتها را همراه می‌آورد و زنجیری محکم نیز در دست داشت. (Abyssos g12)
2 Ya kama macijin, wannan tsohon maciji, wanda yake shi ne Iblis, ko kuwa Shaiɗan, aka kuma ɗaura shi har shekara dubu.
او اژدها را گرفت و به زنجیر کشید و برای مدت هزار سال به چاه بی‌انتها افکند. سپس درِ چاه را بست و قفل کرد، تا در آن هزار سال نتواند هیچ قومی را فریب دهد. پس از گذشت این مدت، اژدها برای مدت کوتاهی باید آزاد گذاشته شود. اژدها، همان مار قدیم است که ابلیس و شیطان نیز نامیده می‌شود. (Abyssos g12)
3 Ya jefa shi cikin Abis, ya kuma kulle ya sa hatimi a kansa, don a hana kada yă ƙara ruɗin al’ummai, sai shekarun nan dubu sun cika. Bayan wannan, dole a sake shi na ɗan lokaci. (Abyssos g12)
4 Na ga kursiyoyi inda waɗanda aka ba su ikon shari’a suke zama a kai. Sai na ga rayukan waɗanda aka yanke kawunansu saboda shaidarsu don Yesu saboda kuma maganar Allah. Ba su yi wa dabban nan ko siffarta sujada ba, ba su kuma sami alamarta a goshinsu ko a hannuwansu ba. Suka sāke rayuwa daga matattu, suka yi mulki tare da Kiristi shekaru dubu.
آنگاه تختهایی دیدم که بر آنها کسانی نشسته بودند که اختیار و قدرت دادرسی به آنها داده شده بود. سپس جانهای کسانی را دیدم که به سبب اعلام پیام عیسی و کلام خدا سرهایشان از تن جدا شده بود. همچنین جانهای آنانی را دیدم که وحش و مجسمه‌اش را نپرستیده بودند و علامتش را بر پیشانی و دست خود نداشتند. اینان همگی، زندگی را از سر نو آغاز کردند و با مسیح هزار سال سلطنت نمودند.
5 (Sauran matattu ba su sāke rayuwa ba, sai da shekaru dubun nan suka cika.) Wannan fa shi ne tashin matattu na farko.
این قیامت اول است. قیامت بعدی در پایان آن هزار سال رخ خواهد داد؛ در آن زمان، بقیهٔ مردگان زنده خواهند شد.
6 Masu albarka da kuma tsarki ne waɗanda suke da rabo a tashin matattu na farko. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kansu, sai dai za su zama firistocin Allah da kuma na Kiristi za su kuma yi mulki tare da shi na shekaru dubu.
خوشبخت و مقدّسند آنانی که در این قیامت اول سهمی دارند. اینان از مرگ دوم هیچ هراسی ندارند، بلکه کاهنان خدا و مسیح بوده، با او هزار سال سلطنت خواهند کرد.
7 Sa’ad da shekaru dubun nan suka cika, za a saki Shaiɗan daga kurkukun da yake,
پس از پایان آن هزار سال، شیطان از زندان آزاد خواهد شد.
8 zai kuma fito don yă ruɗi al’ummai da suke a kursuyoyi huɗu na duniya, Gog da Magog, yă tattara su don yaƙi. Yawansu kuwa ya yi kamar yashi a bakin teku.
او بیرون خواهد رفت تا قومهای جهان یعنی جوج و ماجوج را فریب داده، برای جنگ متحد سازد. آنان سپاه عظیمی را تشکیل خواهند داد که تعدادشان همچون ماسه‌های ساحل دریا بی‌شمار خواهد بود.
9 Suka mamaye duk fāɗin duniya suka kuma kewaye sansanin mutanen Allah, birnin da yake ƙauna. Amma wuta ta fito daga sama ta cinye su.
ایشان در دشت وسیعی، خلق خدا و شهر محبوب اورشلیم را از هر سو محاصره خواهند کرد. اما آتش از آسمان، از سوی خدا خواهد بارید و همه را خواهد سوزاند.
10 Aka jefa Iblis da ya ruɗe su cikin tafkin farar wuta, inda aka jefa dabban nan da annabin ƙaryan nan. Za a ba su azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn g165, Limnē Pyr g3041 g4442)
سپس ابلیس که ایشان را فریب داده بود، به دریاچهٔ آتش افکنده خواهد شد. دریاچهٔ آتش همان جایی است که با گوگرد می‌سوزد و آن وحش و پیامبر دروغین او شبانه روز، تا به ابد، در آنجا عذاب خواهند کشید. (aiōn g165, Limnē Pyr g3041 g4442)
11 Sa’an nan na ga babban farin kursiyi da kuma wannan da yake zama a kansa. Duniya da sararin sama kuwa suka ɓace daga gabansa, babu wuri kuwa dominsu.
آنگاه تخت بزرگ سفیدی را دیدم. بر آن تخت کسی نشسته بود که زمین و آسمان از روی او گریختند و ناپدید شدند.
12 Sai na ga matattu, babba da yaro tsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne littafin rai. Aka yi wa matattu shari’a bisa ga abin da suka aikata yadda yake a rubuce a cikin littattafai.
سپس مرده‌ها را دیدم که از بزرگ و کوچک در برابر خدا ایستاده‌اند. دفترها یکی پس از دیگری گشوده شد تا به دفتر حیات رسید. مردگان همگی بر طبق نوشته‌های این دفترها محاکمه شدند.
13 Teku ya ba da matattu da suke cikinsa, mutuwa da Hades kuma suka ba da matattu da suke cikinsu, aka kuma yi wa kowane mutum shari’a bisa ga abin da ya aikata. (Hadēs g86)
بنابراین، دریا و زمین و قبرها، مرده‌هایی را که در خود داشتند، تحویل دادند تا مطابق اعمالشان محاکمه شوند. (Hadēs g86)
14 Sa’an nan aka jefar da mutuwa da kuma Hades cikin tafkin wuta. Tafkin wutar nan kuwa shi ne mutuwa ta biyu. (Hadēs g86, Limnē Pyr g3041 g4442)
آنگاه مرگ و دنیای مردگان به دریاچهٔ آتش افکنده شد. این است مرگ دوم، یعنی همان دریاچهٔ آتش. (Hadēs g86, Limnē Pyr g3041 g4442)
15 Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a cikin littafin rai ba, an jefar da shi cikin tafkin wutar nan. (Limnē Pyr g3041 g4442)
هر که نامش در دفتر حیات نبود، به دریاچهٔ آتش افکنده شد. (Limnē Pyr g3041 g4442)

< Ru’uya ta Yohanna 20 >