< Ru’uya ta Yohanna 20 >
1 Na kuma ga wani mala’ika yana saukowa daga sama, yana da mabuɗin Abis yana kuma riƙe da ƙaton sarƙa a hannunsa. (Abyssos )
I saw an angel coming down from heaven. He had the key to the deep dark pit, and he was carrying a large chain in his hand. (Abyssos )
2 Ya kama macijin, wannan tsohon maciji, wanda yake shi ne Iblis, ko kuwa Shaiɗan, aka kuma ɗaura shi har shekara dubu.
He seized the dragon. That dragon is the ancient serpent, the devil, that is, Satan. The angel bound him with the chain. That chain could not be loosed {[No one could loose] that chain} for 1,000 years.
3 Ya jefa shi cikin Abis, ya kuma kulle ya sa hatimi a kansa, don a hana kada yă ƙara ruɗin al’ummai, sai shekarun nan dubu sun cika. Bayan wannan, dole a sake shi na ɗan lokaci. (Abyssos )
The angel threw him into the deep dark pit. He shut [the door of the pit], locked it, and sealed it [to prevent anyone from opening it]. He did that in order that Satan might no longer deceive [the people of the] nations [MTY], until those 1,000 years are ended. After that [time], Satan must be released {[God/God’s angel] must release Satan} for a short time [in order that he can do what God has planned]. (Abyssos )
4 Na ga kursiyoyi inda waɗanda aka ba su ikon shari’a suke zama a kai. Sai na ga rayukan waɗanda aka yanke kawunansu saboda shaidarsu don Yesu saboda kuma maganar Allah. Ba su yi wa dabban nan ko siffarta sujada ba, ba su kuma sami alamarta a goshinsu ko a hannuwansu ba. Suka sāke rayuwa daga matattu, suka yi mulki tare da Kiristi shekaru dubu.
I saw thrones on which people were sitting. [They were given] {[God] gave those people} [authority] to judge [other people]. I also saw the souls [of people] whose heads had been {whose heads [others] had} cut off because of [their telling people about] Jesus and declaring God’s message. They were people who refused to worship the beast or its image, and who did not allow [the beast’s agents] to put the beast’s mark on them, either on their foreheads or on their hands. They became alive again, and they ruled with Christ [during those] 1,000 years.
5 (Sauran matattu ba su sāke rayuwa ba, sai da shekaru dubun nan suka cika.) Wannan fa shi ne tashin matattu na farko.
They were the ones who lived again the first time [that God caused dead people] to live again. The rest of [the believers who] had died did not live again until after those 1,000 years.
6 Masu albarka da kuma tsarki ne waɗanda suke da rabo a tashin matattu na farko. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kansu, sai dai za su zama firistocin Allah da kuma na Kiristi za su kuma yi mulki tare da shi na shekaru dubu.
([God] will be pleased with/[How] happy will be) those who live again that first time. God will [consider] them holy. They will not die [PRS] a second time. Instead, they will be priests [who serve] God and Christ, and they will rule with [Christ] during those 1,000 years.
7 Sa’ad da shekaru dubun nan suka cika, za a saki Shaiɗan daga kurkukun da yake,
When the 1,000 years are ended, Satan will be released {[God’s angel] will release Satan} from [the deep pit] in which he was imprisoned.
8 zai kuma fito don yă ruɗi al’ummai da suke a kursuyoyi huɗu na duniya, Gog da Magog, yă tattara su don yaƙi. Yawansu kuwa ya yi kamar yashi a bakin teku.
He will go out to deceive [rebellious] people in nations [IDM] all over the earth. [These are the nations that the prophet Ezekiel called] Gog and Magog. Satan will gather them to fight against [God’s people]. There will be [so many of them fighting against God’s people that no one will be able to count them] [SIM], just like [no one can count the grains of] sand on the ocean shore.
9 Suka mamaye duk fāɗin duniya suka kuma kewaye sansanin mutanen Allah, birnin da yake ƙauna. Amma wuta ta fito daga sama ta cinye su.
They will march over the whole earth and surround the camp of God’s people [in Jerusalem], the city that [God] loves. Then [God will send] fire down from heaven, and it will burn them up.
10 Aka jefa Iblis da ya ruɗe su cikin tafkin farar wuta, inda aka jefa dabban nan da annabin ƙaryan nan. Za a ba su azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn , Limnē Pyr )
The devil, who had deceived those people, will be thrown {[God’s angel] will throw the devil, who had deceived those people} into the lake of burning sulfur. [This is the same lake] into which both the beast and the false prophet had been [thrown] {[he] had [thrown] both the beast and the false prophet}. [As a result], they will continually suffer severely forever. (aiōn , Limnē Pyr )
11 Sa’an nan na ga babban farin kursiyi da kuma wannan da yake zama a kansa. Duniya da sararin sama kuwa suka ɓace daga gabansa, babu wuri kuwa dominsu.
Then I saw a huge white throne on which [God] was sitting. He [was so awesome that] the earth and the sky disappeared from his presence completely; they were completely destroyed {[God] completely destroyed them}.
12 Sai na ga matattu, babba da yaro tsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne littafin rai. Aka yi wa matattu shari’a bisa ga abin da suka aikata yadda yake a rubuce a cikin littattafai.
I saw that the people who had died [but now lived again] were standing in front of the throne. [They included people of] every social status! The books [in which God records what people do] were opened {[God/God’s angel] opened the books [in which God records what people do]}. Another book was opened {[He] opened another book}, which is [called the Book] of Life, [in which God has written the names of people who have eternal life]. [God] judged the people who had died [and now lived again] according to what they had done, just like [he] had recorded it in the books.
13 Teku ya ba da matattu da suke cikinsa, mutuwa da Hades kuma suka ba da matattu da suke cikinsu, aka kuma yi wa kowane mutum shari’a bisa ga abin da ya aikata. (Hadēs )
[The people whose bodies were buried in the] sea [became alive again in order to stand before God’s throne]. Everyone who had been buried on the land (OR, Every person who was waiting in the place where dead people stay) [became alive again, in order to stand before the throne]. [God] judged each one of them according to what each one had done. (Hadēs )
14 Sa’an nan aka jefar da mutuwa da kuma Hades cikin tafkin wuta. Tafkin wutar nan kuwa shi ne mutuwa ta biyu. (Hadēs , Limnē Pyr )
All the unbelievers [PRS, MTY] —those who had been in the place where they waited after they died— [were thrown into the burning lake]. The burning lake is [the place in which people] die the second time. (Hadēs , Limnē Pyr )
15 Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a cikin littafin rai ba, an jefar da shi cikin tafkin wutar nan. (Limnē Pyr )
The people whose [names] [MTY] are not in the book, the one [where God] has written [the names of people who] have [eternal] life, [were also thrown] {([God/God’s angel]) threw them also} [into the lake] of fire. (Limnē Pyr )