< Ru’uya ta Yohanna 2 >
1 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.
Unto the messenger of the assembly, in Ephesus, write: —These things, saith he that holdeth the seven stars in his right hand, he that walketh in the midst of the seven lamps of gold:
2 Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne.
I know thy works, and thy toil, and endurance, and that thou canst not bear bad men, and thou hast tried them who were affirming themselves to be apostles, and they were not, and hast found them false;
3 Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.
And thou hast, endurance, and hast borne for the sake of my name, and hast not grown weary.
4 Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko.
Nevertheless, I have against thee, that, thy first love, thou hast left.
5 Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake.
Remember, therefore, whence thou hast fallen, and repent, and do, thy first works; otherwise, I come unto thee, and will remove thy lamp out of its place, except thou repent.
6 Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.
But, this, thou hast, that thou hatest the works of the Nicolaitanes, which, I also, hate.
7 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.
He that hath an ear, let him hear what, the Spirit, is saying unto the assemblies. Unto him that overcometh—I will give, unto him, to eat of the tree of life, which is in the paradise of God.
8 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.
And, unto the messenger of the assembly, in Smyrna, write: —These things, saith the first and the last, who became dead, and lived:
9 Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne.
I know thy tribulation, and destitution, nevertheless, thou art, rich, and the profane speech from among them who affirm that they themselves are, Jews, and they are not, but a synagogue of Satan.
10 Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
Do not fear the things which thou art about to suffer. Lo! the adversary is about to cast some of you into prison, that ye may be tried, and may have tribulation ten days. Become thou faithful until death, and I will give thee the crown of life.
11 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.
He that hath an ear, let him hear what, the Spirit, is saying unto the assemblies. He that overcometh, shall in nowise be injured by reason of the second death.
12 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.
And, unto the messenger of the assembly, in Pergamum, write: —These things, saith he that hath the sharp, two-edged sword:
13 Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.
I know where thou dwellest, where, the throne of Satan, is; and thou art holding fast my name, and didst not deny my faith, even in the days of Antipas, my witness, my faithful one, who was killed near you, where, Satan, dwelleth.
14 Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci.
Nevertheless, I have against thee, a few things, —that thou hast there, such as hold fast the teaching of Balaam, —who went on to teach Balak to throw a cause of stumbling before the sons of Israel, to eat idol-sacrifices and to commit lewdness:
15 Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa.
thus, even, thou, hast such as hold fast the teaching of the Nicolaitanes, in like manner.
16 Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.
Repent, therefore, otherwise, I come unto thee speedily, —and will fight against them, with the sword of my mouth.
17 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.
He that hath an ear, let him hear what, the Spirit, is saying unto the assemblies. Unto him that overcometh, I will give, unto him, of the hidden manna, and I will give unto him a white stone, and, upon the stone, a new name written, which, no one, knoweth, save he that receiveth it.
18 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.
And, unto the messenger of the assembly, in Thyatira, write: —These things, saith the Son of God, who hath his eyes like a flame of fire, and his feet like unto glowing copper:
19 Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.
I know thy works, and thy love, and faith, and ministry, and endurance, —and that, thy last works, are more than the first.
20 Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka.
Nevertheless, I have against thee, that thou sufferest the woman Jezebel, she who calleth herself a prophetess, and is teaching and leading astray my own servants to commit lewdness and to eat idol-sacrifices;
21 Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya.
and I gave her time, that she might repent, and she willeth not to repent out of her lewdness.
22 Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta.
Lo! I cast her into a bed, and them who are committing adultery with her, into great tribulation, —except they repent out of her works;
23 Zan kashe’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.
and, her children, will I slay with death; —and all the assemblies shall get to know, that, I, am he that searcheth reins and hearts, and will give unto you, each one, according to your works.
24 Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba.
But, unto you, I say, —the rest who are in Thyatira, as many as have not this teaching, such as have not come to know the deep things of Satan, as they say, I do not cast upon you any other burden;
25 Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
nevertheless, what ye have, hold fast, till I shall have come.
26 Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
And, he that overcometh, and keepeth throughout my works, I will, give unto him, authority over the nations;
27 ‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
and he shall shepherd them with a sceptre of iron, —as, vessels of earthenware, are dashed in pieces: —as, I also, have received from my Father.
28 Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
And I will give unto him the morning star.
29 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
He that hath an ear, let him hear what, the Spirit, is saying unto the assemblies.