< Ru’uya ta Yohanna 2 >

1 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.
Andělu Efezské církve piš: Totoť praví ten, kterýž drží těch sedm hvězd v pravici své, jenž se prochází uprostřed těch sedmi svícnů zlatých:
2 Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne.
Známť skutky tvé, a práci tvou, i trpělivost tvou, a že nemůžeš trpěti zlých; a zkusil jsi těch, kteříž se praví býti apoštolé, ale nejsou, a shledals je, že jsou lháři.
3 Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.
A snášel jsi, a trpělivost máš, a pro jméno mé pracovals a neustal.
4 Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko.
Ale mámť něco proti tobě, totiž že jsi tu první lásku svou opustil.
5 Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake.
Protož pomni, odkud jsi vypadl, a čiň pokání a první skutky čiň. Pakliť toho nebude, přijdu na tebe rychle a pohnuť svícnem tvým z místa jeho, nebudeš-li pokání činiti.
6 Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.
Ale toto dobré do sebe máš, že nenávidíš skutků Mikulášenské roty, kterýchž i já nenávidím.
7 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.
Kdo má uši, slyš, co Duch praví církvím: Tomu, kdož zvítězí, dám jísti z dřeva života, kteréž jest uprostřed ráje Božího.
8 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.
Andělu pak Smyrnenské církve piš: Toto praví ten první i poslední, kterýž byl mrtvý, a ožil:
9 Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne.
Vím o skutcích tvých, i o soužení, a chudobě tvé, (ale bohatý jsi), i o rouhání těch, kteříž se praví býti Židé, a nejsou, ale jsou sběř satanova.
10 Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
Nebojž se nic toho, co trpěti máš. Aj, uvržeť ďábel některé z vás do vězení, abyste zkušeni byli, a budete míti úzkost za deset dní. Budiž věrný až do smrti, a dámť korunu života.
11 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.
Kdo má uši, slyš, co Duch praví církvím: Kdo zvítězí, nebude uražen od smrti druhé.
12 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.
Andělu pak Pergamenské církve piš: Totoť praví ten, kterýž má ten meč s obou stran ostrý:
13 Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.
Vím skutky tvé, i kde bydlíš, totiž tu, kdež jest stolice satanova, a že držíš se jména mého, a nezapřel jsi víry mé, ani v těch dnech, když Antipas, svědek můj věrný, zamordován jest u vás, tu, kdež bydlí satan.
14 Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci.
Ale mámť proti tobě něco málo, že tam máš ty, kteříž drží učení Balámovo, jenž učil Baláka pohoršení klásti před obličejem synů Izraelských, aby jedli modlám obětované a smilnili.
15 Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa.
Tak i ty máš některé, kteříž drží učení Mikulášenců, což já v nenávisti mám.
16 Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.
Èiniž pokání. Pakli nebudeš, přijdu na tebe brzy, a bojovatiť budu s nimi mečem úst svých.
17 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.
Kdo má uši, slyšiž, co Duch praví církvím: Tomu, jenž vítězí, dám jísti mannu skrytou a dám jemu kamének bílý, a na tom kaménku jméno nové napsané, kteréhož žádný neví, než ten, kdož je přijímá.
18 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.
Andělu pak Tyatirské církve piš: Totoť praví Syn Boží, jenž má oči jako plamen ohně, a nohy jeho podobné jsou mosazi:
19 Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.
Známť skutky tvé, i lásku, i přisluhování, i věrnost, i trpělivost tvou, a skutky tvé, i ty poslední, kteříž větší jsou nežli první.
20 Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka.
Ale mámť proti tobě něco málo, že dopouštíš ženě Jezábel, kteráž se býti praví prorokyní, učiti a v blud uvoditi služebníky mé, aby smilnili a jedli modlám obětované.
21 Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya.
Ale dalť jsem jí čas, aby pokání činila z smilstva svého, avšak nečinila pokání.
22 Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta.
Aj, já uvrhu ji na lože, i ty, kteříž cizoloží s ní, v soužení převeliké, jestliže nebudou činiti pokání z skutků svých.
23 Zan kashe’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.
A syny její zmorduji smrtí; i zvědíť všecky církve, žeť jsem já ten, kterýž zpytuji ledví a srdce, a odplatím jednomu každému z vás podle skutků vašich.
24 Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba.
Vámť pak pravím i jiným Tyatirským, kteřížkoli nemají učení tohoto, a kteříž nepoznali hlubokosti satanovy, jakž oni říkají: Nevzložímť na vás jiného břemene.
25 Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
Avšak to, což máte, držte, dokavadž nepřijdu.
26 Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
Kdož by pak vítězil a ostříhal až do konce skutků mých, dám jemu moc nad pohany.
27 ‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
I budeť je spravovati prutem železným, a jako nádoba hrnčířova střískáni budou, jakž i já vzal jsem od Otce svého.
28 Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
A dám jemu hvězdu jitřní.
29 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
Kdo má uši, slyš, co Duch praví církvím.

< Ru’uya ta Yohanna 2 >