< Ru’uya ta Yohanna 19 >
1 Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa, “Halleluya! Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,
And after these things, I heard the voice as of a great multitude in heaven, saying, Hallelujah! salvation, and glory, and power, to the Lord our God;
2 gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma. Ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta. Ya rama jinin bayinsa a kanta.”
for his judgments are true and righteous; for he has judged the great harlot, who corrupted the earth with her fornication; and he has avenged the blood of his servants shed by her hand.
3 Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn )
And a second time they said, Hallelujah! And the smoke of her torment ascended for ever and ever. (aiōn )
4 Dattawan nan ashirin da huɗu da halittu huɗun nan masu rai suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, wannan da yake zaune a kursiyi. Suka tā da murya suka ce, “Amin, Halleluya!”
And the twenty-four elders, and the four living creatures fell down and worshiped God, sitting upon the throne, saying, Amen! Hallelujah!
5 Sa’an nan wata murya ta fito daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, dukanku da kuke bayinsa, ku da kuke tsoronsa, babba da yaro!”
And a voice came out from the throne, which said, Praise our God, all you his servants, you that fear him, both small and great.
6 Sai na ji wani abu mai ƙara kamar ƙasaitaccen taron mutane, kamar rurin ruwaye masu gudu da kuma kamar bugun tsawa mai ƙarfi, suna tā da murya suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki ne yake mulki.
And I heard a sound, which was as the voice of a great multitude, and as the voice of many waters, and like the peal of mighty thunderings, saying, Hallelujah! for the Lord God, the Omnipotent, reigns!
7 Bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna mu kuma ɗaukaka shi! Domin lokacin auren Ɗan Ragon ya yi, amaryarsa kuwa ta shirya kanta.
We rejoice, and exult, and give glory to him, because the marriage of the Lamb is come, and his wife has prepared herself.
8 Aka ba ta lallausan lilin, mai haske da tsabta ta sanya.” (Lallausan lilin yana misalta ayyukan adalci na tsarkaka.)
And it was given to her that she should be clothed in fine linen, pure and resplendent; and the fine linen is the righteous acts of the saints.
9 Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta, ‘Masu albarka ne waɗanda aka gayyace su zuwa bikin auren Ɗan Ragon!’” Sai ya ƙara da cewa, “Waɗannan su ne kalmomin Allah da gaske.”
And he said to me, Write--Happy are they who are invited to the marriage supper of the Lamb! And he said to me, These are the true words of God.
10 Da wannan sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada. Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne da kai da kuma’yan’uwanka waɗanda suke riƙe da shaidar Yesu. Ka yi wa Allah sujada! Domin shaidar Yesu ita ce ruhun annabci.”
And I fell before his feet to worship him; and he said to me, See you do it not: I am a fellow-servant with you, and with your brethren who keep the testimony of Jesus. Worship God; for the testimony of Jesus is the spirit of prophecy.
11 Sai na ga sama a buɗe can kuwa a gabana ga farin doki, sunan mahayinsa Mai Aminci da Mai Gaskiya ne. Da adalci yake shari’a yake kuma yaƙi.
And I saw heaven opened, and behold, a white horse; and he that sat upon it was called Faithful and True; and he judges and makes war in righteousness:
12 Idanunsa sun yi kamar harshen wuta, a kansa kuwa akwai rawani masu yawa. Yana da suna rubuce a kansa da babu wanda ya sani sai dai shi.
whose eyes are as a flame of fire; and many diadems were upon his head, having a name written which no man knows but himself:
13 Yana saye da rigar da aka tsoma a jini, sunansa kuwa Kalman Allah ne.
and he was clothed in a garment dipt in blood, and his name is called THE WORD OF GOD.
14 Mayaƙan sama suna biye da shi, suna hawan fararen dawakai, saye da fararen tufafi masu tsabta na lallausan lilin.
And the armies which are in heaven followed him, riding on white horses, clothed in fine linen, white and clean.
15 Daga bakinsa takobi mai kaifi ya fito. Da shi zai karkashe al’ummai. “Zai yi mulkinsu da sandan sarautar ƙarfe.” Yana tattake wurin matsin ruwan inabi na fushin Allah Maɗaukaki.
And there went out of his mouth a sharp sword, that with it he might smite the nations: and he shall govern them with a rod of iron; and he treads the wine press of the indignation and wrath of almighty God.
16 A rigarsa da kuma a cinyarsa akwai wannan suna a rubuce, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji.
And he has upon his garment and his thigh a name written-- KING OF KINGS, AND LORD OF LORDS.
17 Na kuma ga wani mala’ika tsaye a cikin rana, wanda ya yi kira da babbar murya ga dukan tsuntsaye da suke tashi sama a tsakiyar sararin sama cewa, “Ku zo, ku taru don babban bikin nan na Allah,
And I saw a single angel standing in the sun; and he cried with a loud voice, saying to all the birds of prey, which were flying in the midst of heaven, Come, and assemble yourselves to the great supper of God:
18 don ku ci naman sarakuna, jarumawa, da kuma manyan mutane, na dawakai da mahayansu, da kuma naman dukan mutane,’yantacce da bawa, babba da yaro.”
that you may eat the flesh of kings, and the flesh of commanders, and the flesh of the mighty, and the flesh of horses, and of those that sat on them; and the flesh of all, both freemen and slaves, both small and great.
19 Sa’an nan na ga dabbar da sarakunan duniya da mayaƙansu sun taru don su yi yaƙi da wannan wanda yake kan farin dokin da kuma mayaƙansa.
And I saw the beast, and the kings of the earth, and their armies gathered together to make war with him who sits upon the white horse, and with his army.
20 Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr )
And the beast was taken captive, and with him the false prophet, who had wrought signs before him, by which he deceived those who received the mark of the beast, and those who worshiped his image; both of whom were cast alive into the lake of fire which burned with brimstone. (Limnē Pyr )
21 Sauran kuma aka kashe su da takobin da ya fito daga bakin wannan wanda yake kan dokin. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu iyakar iyawarsu.
And the rest were slain with the sword that came out of the mouth of him who sat on the horse: and all the birds were satiated with their flesh.