< Ru’uya ta Yohanna 19 >

1 Bayan wannan sai na ji abin da ya yi kamar ƙasaitaccen taron mutane a sama, suna cewa, “Halleluya! Ceto da ɗaukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu,
这之后,我听见天上好像有一大群人的喧闹声:“哈利路亚!救恩、荣耀、权能都属于我们的上帝,
2 gama hukuncinsa daidai ne, mai adalci kuma. Ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta ɓata duniya da zinace zinacenta. Ya rama jinin bayinsa a kanta.”
因为他的审判是真实正义的;因为他审判了那臭名昭著、以淫乱败坏世界的淫妇;并因为那淫妇谋害其仆人而对其进行判决。”
3 Suka sāke tā da murya suka ce, “Halleluya! Hayaƙin yake fitowa daga wurinta ya yi ta tashi sama har abada abadin.” (aiōn g165)
他们又喊了一次:“哈利路亚!她的毁灭所产生的浓烟永远升腾。” (aiōn g165)
4 Dattawan nan ashirin da huɗu da halittu huɗun nan masu rai suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, wannan da yake zaune a kursiyi. Suka tā da murya suka ce, “Amin, Halleluya!”
那二十四位长老和四个活物,俯伏敬拜坐在宝座上的上帝,喊道:“阿门!哈利路亚!”
5 Sa’an nan wata murya ta fito daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, dukanku da kuke bayinsa, ku da kuke tsoronsa, babba da yaro!”
接宝座传出声音,说:“所有上帝的仆人哪!凡是尊重他的,无论大小,都应当赞美我们的上帝!”
6 Sai na ji wani abu mai ƙara kamar ƙasaitaccen taron mutane, kamar rurin ruwaye masu gudu da kuma kamar bugun tsawa mai ƙarfi, suna tā da murya suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki ne yake mulki.
又听见一个声音,好像是一大群人,如奔流的水,又像惊雷,说:“哈利路亚!因为主、我们全能的上帝统治了!
7 Bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna mu kuma ɗaukaka shi! Domin lokacin auren Ɗan Ragon ya yi, amaryarsa kuwa ta shirya kanta.
让我们欢喜庆祝,把荣耀归给他!因为羊羔的婚期到了;他的新娘也自己预备好了。”
8 Aka ba ta lallausan lilin, mai haske da tsabta ta sanya.” (Lallausan lilin yana misalta ayyukan adalci na tsarkaka.)
她得到了干净的白色细麻衣,(细麻衣代表着信徒的好工作)
9 Sai mala’ikan ya ce mini, “Rubuta, ‘Masu albarka ne waɗanda aka gayyace su zuwa bikin auren Ɗan Ragon!’” Sai ya ƙara da cewa, “Waɗannan su ne kalmomin Allah da gaske.”
天使对我说:“写下来:‘受邀参加羊羔婚筵的人太幸福了!’”他又对我说:“这都是上帝真实说的话。”
10 Da wannan sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada. Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne da kai da kuma’yan’uwanka waɗanda suke riƙe da shaidar Yesu. Ka yi wa Allah sujada! Domin shaidar Yesu ita ce ruhun annabci.”
我就俯伏在天使脚前要拜他。但他对我说:“不可以这样!我和你以及那些接受耶稣作见证的人一样,都是上帝的仆人。敬拜上帝,因为耶稣的证言就是预言的灵。”
11 Sai na ga sama a buɗe can kuwa a gabana ga farin doki, sunan mahayinsa Mai Aminci da Mai Gaskiya ne. Da adalci yake shari’a yake kuma yaƙi.
我看着天打开了。有一匹白马站在那里,骑士叫做“忠信”和“真实”,当他审判,他是正义的;当他战斗,他是正义的。
12 Idanunsa sun yi kamar harshen wuta, a kansa kuwa akwai rawani masu yawa. Yana da suna rubuce a kansa da babu wanda ya sani sai dai shi.
他的眼睛好像火焰,头上戴着许多皇冠,身上写着一个名字除了他自己没有人认识。
13 Yana saye da rigar da aka tsoma a jini, sunansa kuwa Kalman Allah ne.
他身穿一件浸过血的衣服,他的名字叫做“上帝之道。”
14 Mayaƙan sama suna biye da shi, suna hawan fararen dawakai, saye da fararen tufafi masu tsabta na lallausan lilin.
天上的众军都骑着白马,穿著洁白的细麻衣,跟随他。
15 Daga bakinsa takobi mai kaifi ya fito. Da shi zai karkashe al’ummai. “Zai yi mulkinsu da sandan sarautar ƙarfe.” Yana tattake wurin matsin ruwan inabi na fushin Allah Maɗaukaki.
他口中吐出一把利剑,用于击打列国。他将用铁杖治理他们,他自己还要在全能上帝审判的压酒池踩葡萄。
16 A rigarsa da kuma a cinyarsa akwai wannan suna a rubuce, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji.
在他的长袍和大腿上,写着“万王之王,万主之主”的名号。
17 Na kuma ga wani mala’ika tsaye a cikin rana, wanda ya yi kira da babbar murya ga dukan tsuntsaye da suke tashi sama a tsakiyar sararin sama cewa, “Ku zo, ku taru don babban bikin nan na Allah,
我又看见一位天使站在太阳中,向高空所有的飞鸟大声呼喊:“来吧!聚集起来赴上帝的伟大宴席!
18 don ku ci naman sarakuna, jarumawa, da kuma manyan mutane, na dawakai da mahayansu, da kuma naman dukan mutane,’yantacce da bawa, babba da yaro.”
这里可以吃死人的肉:君王、领袖、壮士、还有马和骑士,以及无论是自由的、作奴隶的、伟大的、渺小的,吃所有人的肉。”
19 Sa’an nan na ga dabbar da sarakunan duniya da mayaƙansu sun taru don su yi yaƙi da wannan wanda yake kan farin dokin da kuma mayaƙansa.
我看见那野兽和地上的国王,还有他们的众军,都集合起来,要跟那马背骑士和他的军队作战。
20 Amma aka kama dabbar tare da annabin ƙaryan nan wanda ya aikata alamu masu banmamaki a madadinta. Da waɗannan alamun ne ya ruɗe waɗanda suka sami alamar dabbar suka kuma bauta wa siffarta. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin wuta ta da farar wuta mai ci. (Limnē Pyr g3041 g4442)
那野兽被捉住了;连同在兽面前做出奇事的假先知(通过这种方式,他欺骗那些接受了野兽记号、膜拜野兽像的人)。他们都被活活拋在烧着硫磺的火湖里去。 (Limnē Pyr g3041 g4442)
21 Sauran kuma aka kashe su da takobin da ya fito daga bakin wannan wanda yake kan dokin. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu iyakar iyawarsu.
其余的人都被那白马骑士口中吐出来的剑杀了,他们的肉让飞鸟吃饱了。

< Ru’uya ta Yohanna 19 >