< Ru’uya ta Yohanna 18 >
1 Bayan wannan sai na ga wani mala’ika yana saukowa daga sama. Yana da iko mai girma, aka haskaka duniya da darajarsa.
After this I saw another angel, descending from Heaven, invested with great authority; and the earth was illuminated by his splendour.
2 Ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi. Ta zama gidan aljanu da kuma wurin zaman kowace irin mugun ruhu, wurin zaman kowane irin tsuntsu marar tsabta da mai banƙyama.
With a mighty voice he cried — ‘She has fallen! She has fallen — Babylon the Great! She has become an abode of demons, a stronghold of every wicked spirit, a stronghold of every foul and hateful bird.
3 Gama dukan al’ummai sun sha ruwan inabin haukan zinace zinacenta. Sarakunan duniya sun yi zina tare da ita, attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”
For, after drinking the maddening wine of her licentiousness, all the nations have fallen; while all the kings of the earth have had licentious intercourse with her, and the merchants of the earth have grown rich through the excess of her luxury.’
4 Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fita daga cikinta, mutanena, don kada zunubanta su shafe ku, don kada wata annobarta ta same ku;
Then I heard another voice from Heaven saying — ‘Come out of her, my People, that you may not participate in her sins, and that you may not suffer from the Curses inflicted upon her.
5 gama zunubanta sun yi tsororuwa sun kai sama. Allah kuma ya tuna da laifofinta.
For her sins are heaped up to the heavens, and God has not forgotten her misdeeds.
6 Ku sāka mata kamar yadda ta sāka muku; ku sāka mata sau biyu na abin da ta yi. Ku dama mata sau biyu na abin da yake cikin kwaf nata.
Pay her back the treatment with which she has treated you; yes, repay twice over what her actions deserve; in the cup which she mixed for you, mix for her as much again;
7 Ku ba ta isashen azaba da baƙin ciki kamar daraja da kuma jin daɗin da ta ba wa kanta. A zuciyarta takan yi taƙama, ta ce, ‘Ina zama kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taɓa yin makoki ba.’
for her self-glorification and her luxury, give her now an equal measure of torture and misery. In her heart she says ‘I sit here a queen; no widow am I; I shall never know misery.’
8 Saboda haka a rana ɗaya annobarta za su cim mata, mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta zai cinye ta, gama Ubangiji Allah mai girma ne, wanda yake shari’anta ta.
Therefore in one day shall these Curses befall her — death, misery, and famine, and she shall be utterly consumed by fire; for mighty is the Lord God who condemned her.
9 “Sa’ad da sarakunan duniya da suka yi zina da ita suka kuma yi tarayya cikin jin daɗinta suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi kuka da makoki saboda ita.
All the kings of the earth who had licentious intercourse with her and shared her luxury will weep and lament over her, when they see the smoke from the burning city,
10 Don tsoron ganin azabarta za su tsaya daga nesa, su yi kuka suna cewa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma. Ya ke Babilon, birni mai iko! Cikin sa’a guda hallakarki ta zo!’
while they stand at a distance, horrified at her torture, and cry — ‘Alas! Alas! Great City! O mighty City of Babylon! In a single hour your judgment fell.
11 “Attajiran duniya za su yi kuka su kuma yi makoki a kanta, domin ba wanda yake ƙara sayen kayayyakinsu
And the merchants of the earth weep and wail over her, because no longer does any one buy their cargoes —
12 kayayyakin zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja da lu’ulu’ai; lallausan lilin, tufa masu ruwan shunayya, siliki da jan tufa; da kowane irin katakai masu ƙanshi da kayayyaki na kowane iri da aka yi da hauren giwa, katakai masu tsada, tagulla, baƙin ƙarfe da dutse mai sheƙi;
their cargoes of gold, or silver, or precious stones, or pearls, or fine linen, or purple robes, or silk, or scarlet cloth; nor their many scented woods; nor their many articles of ivory; nor their many articles of choicest wood, or brass, or iron, or marble;
13 kayayyakin sinnamon da kayan yaji, na turaren wuta, mur da turare, na ruwan inabi da man zaitun, na gari mai laushi da alkama; shanu da tumaki; dawakai da kekunan doki, da jikuna da kuma rayukan mutane.
nor their cinnamon, or spice, or incense, or perfumes, or frankincense, or wine, or oil, or fine flour, or wheat, or cattle, or sheep; nor their horses, or chariots, or slaves; nor the bodies and souls of men.
14 “Za su ce, ‘Amfanin da kike marmari ya kuɓuce. Dukan arzikinki da darajarki sun ɓace, ba kuwa za a ƙara samunsu ba.’
The fruit that your soul craved is no longer within your reach, and all dainties and luxuries are lost to you, never to be found again.’
15 Attajiran da suka sayar da waɗannan kayayyaki suka kuma sami arzikinsu daga gare ta za su tsaya daga nesa, cike da tsoron ganin azabarta. Za su yi kuka da makoki
The merchants who sold these things, and grew rich by her, will stand at a distance weeping and wailing, horrified at her torture, and crying —
16 su ce, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, saye da lallausan lilin, shunayya da kuma ja, mai walƙiya da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai!
‘Alas! Alas! Great City! O City clothed in fine linen, and purple, and scarlet cloth! O City adorned with gold ornaments, and precious stones, and pearls!
17 Cikin sa’a guda irin wannan dukiya mai yawa ta hallaka!’ “Duk matuƙan jirgin ruwa, da dukan waɗanda suke tafiya a jirgin ruwa, ma’aikatanta, da duk masu samun abin zama gari daga teku za su tsaya daga nesa.
In a single hour your vast wealth vanished.’ Every ship’s captain and all who sail to any port, and sailors, and all who get their living from the sea, stood at a distance,
18 Sa’ad da suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi ihu su ce, ‘An taɓa samun birni kamar wannan babban birnin kuwa?’
and seeing the smoke from the burning city, cried — ‘What city can compare with the Great City?’
19 Za su zuba ƙura a kawunansu, da kuka da makoki za su yi ta kururuwa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, inda dukan waɗanda suke da jiragen ruwa a teku suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa! Cikin sa’a ɗaya ta hallaka!’
They threw dust on their heads, and, as they wept and wailed, they cried — ‘Alas! Alas! Great City! All who have ships on the sea grew rich through her magnificence. In a single hour it has vanished.’
20 “Ki yi murna a kanta, ya sama! Ku yi murna, ku tsarkaka! Ku yi murna, ku manzanni da annabawa! Allah ya hukunta shi saboda abin da ya yi muku.”
Rejoice over her, O Heaven, and People of Christ, and Apostles, and Prophets, for God has avenged you on her!
21 Sa’an nan wani mala’ika mai ƙarfi ya ɗauki dutse kamar girman babban dutsen niƙa ya jefa cikin teku ya ce, “Da wannan irin giggitawa za a jefar da birnin Babilon mai girma ƙasa, ba za a ƙara ganin ta ba.
Then a mighty angel took up a stone like a great millstone, and threw it into the sea, crying — ‘So shall Babylon, the Great City, be violently overthrown, never more to be seen.
22 Ba za a ƙara jin ƙarar kiɗin masu garaya da muryar mawaƙa, da na masu bushe-bushe, da na masu busan ƙaho a cikinki ba. Ba za a ƙara samun ma’aikaci na kowace irin sana’a a cikinki kuma ba. Ba za a ƙara jin ƙarar dutsen niƙa a cikinki kuma ba.
No more shall the music of harpers, or minstrels, or flute players, or trumpeters be heard in you, no more shall any worker, skilled in any art, be found in you; no more shall the sound of a mill be heard in you;
23 Hasken fitila ba zai ƙara haskakawa a cikinki ba. Ba za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba. Attajiranki, dā su ne manyan mutanen duniya. Ta wurin sihirinki, dukan ƙasashe sun kauce.
no more shall the light of a lamp shine in you; no more shall the voices of bridegroom and bride be heard in you. Your merchants were the great men of the earth, for all the nations were deceived by your magical charms.
24 A cikinta aka sami jinin annabawa, da na tsarkaka, da kuma na dukan waɗanda aka kashe a duniya.”
Yes, and in her was to be found the blood of the Prophets and of Christ’s People, and of all who have been put to death upon the earth.’