< Ru’uya ta Yohanna 18 >
1 Bayan wannan sai na ga wani mala’ika yana saukowa daga sama. Yana da iko mai girma, aka haskaka duniya da darajarsa.
And after these thinges, I sawe another Angel come downe from heauen, hauing great power, so that the earth was lightened with his glorie,
2 Ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi. Ta zama gidan aljanu da kuma wurin zaman kowace irin mugun ruhu, wurin zaman kowane irin tsuntsu marar tsabta da mai banƙyama.
And he cryed out mightily with a loud voyce, saying, It is fallen, it is fallen, Babylon that great citie, and is become the habitation of deuils, and the holde of all foule spirits, and a cage of euery vncleane and hatefull birde.
3 Gama dukan al’ummai sun sha ruwan inabin haukan zinace zinacenta. Sarakunan duniya sun yi zina tare da ita, attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”
For all nations haue drunken of the wine of the wrath of her fornication, and the Kings of the earth haue committed fornication with her, and the marchants of the earth are waxed rich of the abundance of her pleasures.
4 Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fita daga cikinta, mutanena, don kada zunubanta su shafe ku, don kada wata annobarta ta same ku;
And I heard another voyce from heauen say, Goe out of her, my people, that ye be not partakers of her sinnes, and that ye receiue not of her plagues.
5 gama zunubanta sun yi tsororuwa sun kai sama. Allah kuma ya tuna da laifofinta.
For her sinnes are come vp into heauen, and God hath remembred her iniquities.
6 Ku sāka mata kamar yadda ta sāka muku; ku sāka mata sau biyu na abin da ta yi. Ku dama mata sau biyu na abin da yake cikin kwaf nata.
Rewarde her, euen as she hath rewarded you, and giue her double according to her workes: and in the cup that she hath filled to you, fill her ye double.
7 Ku ba ta isashen azaba da baƙin ciki kamar daraja da kuma jin daɗin da ta ba wa kanta. A zuciyarta takan yi taƙama, ta ce, ‘Ina zama kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taɓa yin makoki ba.’
In as much as she glorified her selfe, and liued in pleasure, so much giue ye to her torment and sorow: for she saith in her heart, I sit being a queene, and am no widowe, and shall see no mourning.
8 Saboda haka a rana ɗaya annobarta za su cim mata, mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta zai cinye ta, gama Ubangiji Allah mai girma ne, wanda yake shari’anta ta.
Therefore shall her plagues come at one day, death, and sorowe, and famine, and she shalbe burnt with fire: for that God which condemneth her, is a strong Lord.
9 “Sa’ad da sarakunan duniya da suka yi zina da ita suka kuma yi tarayya cikin jin daɗinta suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi kuka da makoki saboda ita.
And the kings of the earth shall bewayle her, and lament for her, which haue committed fornication, and liued in pleasure with her, when they shall see that smoke of that her burning,
10 Don tsoron ganin azabarta za su tsaya daga nesa, su yi kuka suna cewa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma. Ya ke Babilon, birni mai iko! Cikin sa’a guda hallakarki ta zo!’
And shall stand a farre off for feare of her torment, saying, Alas, alas, that great citie Babylon, that mightie citie: for in one houre is thy iudgement come.
11 “Attajiran duniya za su yi kuka su kuma yi makoki a kanta, domin ba wanda yake ƙara sayen kayayyakinsu
And the marchants of the earth shall weepe and wayle ouer her: for no man byeth their ware any more.
12 kayayyakin zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja da lu’ulu’ai; lallausan lilin, tufa masu ruwan shunayya, siliki da jan tufa; da kowane irin katakai masu ƙanshi da kayayyaki na kowane iri da aka yi da hauren giwa, katakai masu tsada, tagulla, baƙin ƙarfe da dutse mai sheƙi;
The ware of golde, and siluer, and of precious stone, and of pearles, and of fine linnen, and of purple, and of silke, and of skarlet, and of all maner of Thyne wood, and of all vessels of yuorie, and of all vessels of most precious wood, and of brasse, and of yron, and of marble,
13 kayayyakin sinnamon da kayan yaji, na turaren wuta, mur da turare, na ruwan inabi da man zaitun, na gari mai laushi da alkama; shanu da tumaki; dawakai da kekunan doki, da jikuna da kuma rayukan mutane.
And of cinamon, and odours, and ointments, and frankincense, and wine, and oyle, and fine floure, and wheate, and beastes, and sheepe, and horses, and charets, and seruants, and soules of men.
14 “Za su ce, ‘Amfanin da kike marmari ya kuɓuce. Dukan arzikinki da darajarki sun ɓace, ba kuwa za a ƙara samunsu ba.’
(And the apples that thy soule lusted after, are departed from thee, and all things which were fatte and excellent, are departed from thee, and thou shalt finde them no more)
15 Attajiran da suka sayar da waɗannan kayayyaki suka kuma sami arzikinsu daga gare ta za su tsaya daga nesa, cike da tsoron ganin azabarta. Za su yi kuka da makoki
The marchants of these thinges which were waxed riche, shall stand a farre off from her, for feare of her torment, weeping and wayling,
16 su ce, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, saye da lallausan lilin, shunayya da kuma ja, mai walƙiya da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai!
And saying, Alas, alas, that great citie, that was clothed in fine linnen and purple, and skarlet, and gilded with gold, and precious stones, and pearles.
17 Cikin sa’a guda irin wannan dukiya mai yawa ta hallaka!’ “Duk matuƙan jirgin ruwa, da dukan waɗanda suke tafiya a jirgin ruwa, ma’aikatanta, da duk masu samun abin zama gari daga teku za su tsaya daga nesa.
For in one houre so great riches are come to desolation. And euery shipmaster, and all the people that occupie shippes, and shipmen, and whosoeuer traffike on the sea, shall stand a farre off,
18 Sa’ad da suka ga hayaƙin ƙunarta, za su yi ihu su ce, ‘An taɓa samun birni kamar wannan babban birnin kuwa?’
And crie, when they see that smoke of that her burning, saying, What citie was like vnto this great citie?
19 Za su zuba ƙura a kawunansu, da kuka da makoki za su yi ta kururuwa, “‘Kaito! Kaito, ya birni mai girma, inda dukan waɗanda suke da jiragen ruwa a teku suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa! Cikin sa’a ɗaya ta hallaka!’
And they shall cast dust on their heads, and crie, weeping, and wayling, and say, Alas, alas, that great citie, wherein were made rich all that had ships on the sea by her costlinesse: for in one houre she is made desolate.
20 “Ki yi murna a kanta, ya sama! Ku yi murna, ku tsarkaka! Ku yi murna, ku manzanni da annabawa! Allah ya hukunta shi saboda abin da ya yi muku.”
O heauen, reioyce of her, and ye holy Apostles and Prophets: for God hath punished her to be reuenged on her for your sakes.
21 Sa’an nan wani mala’ika mai ƙarfi ya ɗauki dutse kamar girman babban dutsen niƙa ya jefa cikin teku ya ce, “Da wannan irin giggitawa za a jefar da birnin Babilon mai girma ƙasa, ba za a ƙara ganin ta ba.
Then a mightie Angell tooke vp a stone like a great milstone, and cast it into the sea, saying, With such violence shall that great citie Babylon be cast, and shalbe found no more.
22 Ba za a ƙara jin ƙarar kiɗin masu garaya da muryar mawaƙa, da na masu bushe-bushe, da na masu busan ƙaho a cikinki ba. Ba za a ƙara samun ma’aikaci na kowace irin sana’a a cikinki kuma ba. Ba za a ƙara jin ƙarar dutsen niƙa a cikinki kuma ba.
And the voyce of harpers, and musicians, and of pipers, and trumpetters shalbe heard no more in thee, and no craftesman, of whatsoeuer craft he be, shall be found any more in thee: and the sound of a milstone shalbe heard no more in thee.
23 Hasken fitila ba zai ƙara haskakawa a cikinki ba. Ba za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba. Attajiranki, dā su ne manyan mutanen duniya. Ta wurin sihirinki, dukan ƙasashe sun kauce.
And the light of a candle shall shine no more in thee: and the voyce of the bridegrome and of the bride shalbe heard no more in thee: for thy marchants were the great men of the earth: and with thine inchantments were deceiued all nations.
24 A cikinta aka sami jinin annabawa, da na tsarkaka, da kuma na dukan waɗanda aka kashe a duniya.”
And in her was found the blood of the Prophets, and of the Saints, and of all that were slaine vpon the earth.