< Ru’uya ta Yohanna 17 >

1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
One of the seven angels, who had [one of] the seven bowls, came to me. He said to me, “Come [with me], and I will show you how [God] will punish the very evil [city that is represented by] [SYM] a prostitute, a city in which there are many canals [of] water.
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
[It is as though] the rulers of earth have acted immorally [and idolatrously] with the people of that city [MET], and they [have persuaded people] who live on the earth to act immorally [and idolatrously] with them [MET], [just like a prostitute persuades men to drink] the [strong] wine [she gives them, resulting in their] becoming drunk [and] then committing sexual immorality. with her.”
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
Then, as [God’s] Spirit [controlled me], the angel carried me away to a desolate area. There I saw a woman who was sitting on a red beast. The beast had names [written] all over itself. They were names that (insulted/spoke evil against) [God]. The beast had seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
The woman [that I saw] was wearing purple and red [clothes]; and gold, precious stones, and pearls were fastened to her [clothes and her body]. She held in her hand a golden cup. The cup was full of [a liquid that represents] [SYM] the detestable/disgusting, idolatrous things and filthy immoral things that she [does].
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
This name, that has a hidden/secret [meaning], was written on her forehead: “[This woman is] Babylon, the very evil [city! She acts like] the mother of the prostitutes on the earth. She teaches them to [act] immorally and to worship idols.”
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
I saw that the woman had become drunk as a result of drinking the blood of God’s people, those who had told others about Jesus. When I saw her, I was very bewildered/perplexed.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
The angel said to me, “Do not be bewildered [RHQ]! I will explain to you the hidden/secret meaning of the woman and of the beast on which she rides, the beast that has the seven heads and the ten horns.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos g12)
The beast that you saw [lived] previously. Eventually God will destroy him, but now he is dead. He is [about to] come up (from the underworld/from the deep dark pit). [When] the beast who had previously lived, and who then had died, reappears, the people who live on the earth will be amazed. [They are people whose] names were not in the book in which are written the names of people [who will] have eternal life. [The angels have been writing those names in a list] (from the beginning of the world/from the time when the world began). (Abyssos g12)
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
Those who [think] wisely [can understand] this: The seven heads [of the beast] on which the woman sits [symbolize] the seven hills [of the city that the woman represents]. They also [symbolize] seven rulers.
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
Five [of those rulers] have died. One is [still alive]. The seventh [ruler] has not yet come. When he comes, he must remain on earth for [only] a short [time].
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
The beast that [lived] before and then was not [alive] will be the eighth [ruler]. He will be [evil like] the seven [rulers were, but God] will surely destroy him.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
The ten horns that you saw [represent] ten rulers who have not yet begun to rule. They, together with the beast, will be authorized to rule [people for only a short time, as if it were] [MET] for one hour.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
Those [rulers] will all agree to do the same thing. [As a result] they will give to the beast their power [to rule people] as well as their authority [to rule people] [DOU].
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
The rulers and the beast will fight against [Jesus], the [one who is like a] lamb. He will defeat them, because he is Lord [who rules over all other] lords and the King [who rules over all other] kings. Those [people] who are with [and helping him] are the ones whom [God] has chosen, and who keep [serving him] faithfully.”
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
Then the angel said to me, “The waters that you saw in the city where the prostitute sits represent people-[groups], multitudes [of people], nations, and [speakers of many languages] [MTY].
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
The ten horns that you saw [represent rulers] [SYM]. They and the beast will hate [the people in the city] [MTY] that the prostitute [represents]. As a result, they will [take away everything that is in the city, as if] they were [MET] leaving it naked. They will [destroy it as if] [MET] devouring flesh/meat, and they will burn it with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
They will do that because God has caused them to decide to do what he wants them to do. As a result, they will let the beast have their power to rule until what God has said is fulfilled {until [they] fulfill what God has said} [MTY].
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
The prostitute that you saw [represents] the very evil city [whose leaders] [MTY] rule over the kings of the earth.”

< Ru’uya ta Yohanna 17 >