< Ru’uya ta Yohanna 17 >

1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
Then one of the seven angels who had the seven bowls came and said to me, “Come, I will show yoʋ the judgment of the great prostitute who sits on many waters.
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
With her the kings of the earth have committed fornication, and those who dwell on the earth have become drunk with the wine of her fornication.”
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
So he carried me away in the Spirit to a wilderness, and I saw a woman sitting on a scarlet beast, the one that was full of blasphemous names and had seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
The woman was clothed in purple and scarlet, and adorned with gold, precious stones, and pearls. She held in her hand a golden cup full of abominations and the filth of the fornication of the earth.
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
A mysterious name was written on her forehead: “Babylon the great, the mother of prostitutes and of the abominations of the earth.”
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
And I saw the woman drunk with the blood of the saints, the blood of the martyrs of Jesus. When I saw her, I was greatly amazed.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
But the angel said to me, “Why are yoʋ so amazed? I will tell yoʋ the mystery of the woman and of the beast with seven heads and ten horns that carries her.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos g12)
The beast that yoʋ saw was, and is not, and is about to come up out of the abyss and go to destruction. Those who dwell on the earth, whose names have not been written in the book of life from the foundation of the world, will be amazed when they see that the beast was and is not and will be back. (Abyssos g12)
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
This calls for a mind that has wisdom: The seven heads are seven mountains on which the woman sits.
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
They are also seven kings. Five have fallen, one is, and another has not yet come; but when he does come, he must remain for only a little while.
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
The beast that was and is not, is an eighth king. Yet he is one of the seven and is on his way to destruction.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
The ten horns that yoʋ saw are ten kings who have not yet received a kingdom, but they will receive authority as kings for one hour with the beast.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
These kings have one mind and will give their power and authority to the beast.
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
They will make war with the Lamb, but the Lamb will conquer them because he is the Lord of lords and King of kings, and those with him are called, chosen, and faithful.”
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
Then the angel said to me, “The waters yoʋ saw, where the prostitute sits, are peoples, multitudes, nations, and tongues.
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
The beast and the ten horns yoʋ saw will hate the prostitute. They will make her desolate and naked; they will eat her flesh and burn her with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
For God has put it into their hearts to carry out his purpose by being of one mind and handing their kingdom over to the beast until the words of God are fulfilled.
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
As for the woman yoʋ saw, she is the great city that has dominion over the kings over the earth.”

< Ru’uya ta Yohanna 17 >