< Ru’uya ta Yohanna 17 >

1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
And one of the seven messengers who had the seven bowls came, and spake with me, saying—Hither! I will point out to thee the judgment of the great harlot, who sitteth upon many waters,
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
with whom the kings of the earth committed lewdness, —and they who were dwelling upon the earth were made drunk with the wine of her lewdness.
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And he carried me away into a desert, in spirit. And I saw a woman, sitting upon a scarlet wild-beast full of names of blasphemy, having seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
And, the woman, was arrayed with purple and scarlet, and decked with gold and precious stone and pearls, —having a cup of gold in her hand, full of abominations and the impurities of her lewdness;
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
and, upon her forehead, a name written, a secret: Babylon the great, the Mother of the Harlots and of the Abominations of the earth.
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
And I saw the woman, drunk with the blood of the saints, and with the blood of the witnesses of Jesus. And I was astonished, when I beheld her, with great astonishment.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And the messenger said unto me—Wherefore wast thou astonished? I, will tell thee the secret of the woman, and of the wild-beast that carrieth her, which hath the seven heads and the ten horns.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos g12)
The wild-beast which thou sawest, was, and is not, and is about to come up out of the abyss, and into, destruction, goeth away. And they who are dwelling upon the earth whose name is not written upon the book of life from the foundation of the world, will be astonished, when they see the wild-beast, because it was, and is not, and shall be present. (Abyssos g12)
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
Here, is the mind that hath wisdom. The seven heads, are, seven mountains, whereupon the woman sitteth;
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
and they are, seven kings: the five, have fallen, the one, is, the other, hath not yet come; and, whensoever he shall come, a little while, must he remain,
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
and the wild-beast which was and is not. And he, is an eighth, and is, of the seven, —and, into destruction, goeth away.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
And, the ten horns which thou sawest, are, ten kings, —who, indeed, have not received, sovereignty, as yet, but, authority, as kings, for one hour, shall receive, with the wild-beast.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
These, have, one mind, and, their power and authority, unto the wild-beast, they give.
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
These, with the Lamb, will make war; and, the Lamb, will overcome them, because he is, Lord of lords, and King of kings, —and, they who are with him, are called and chosen and faithful.
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
And he saith unto me—The waters which thou sawest, where the harlot sitteth, are, peoples and multitudes, and nations and tongues.
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
And the ten horns which thou sawest, and the wild-beast, these, shall hate the harlot, and, desolate, shall make her, and naked, and, her flesh, shall they eat, and, herself, shall they burn up with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
For, God, hath put into their hearts, to do his mind, and to do one mind, —and to give their sovereignty unto the wild-beast, until the words of God shall be completed.
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
And, the woman whom thou sawest, is the great city, which hath sovereignty over the kings of the earth.

< Ru’uya ta Yohanna 17 >