< Ru’uya ta Yohanna 17 >
1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
And there came one of the seven angels, who had the seven vials, and spoke with me, saying: Come, I will shew thee the condemnation of the great harlot, who sitteth upon many waters,
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
With whom the kings of the earth have committed fornication; and they who inhabit the earth, have been made drunk with the whine of her whoredom.
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And he took me away in spirit into the desert. And I saw a woman sitting upon a scarlet coloured beast, full of names of blasphemy, having seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
And the woman was clothed round about with purple and scarlet, and gilt with gold, and precious stones and pearls, having a golden cup in her hand, full of the abomination and filthiness of her fornication.
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
And on her forehead a name was written: A mystery; Babylon the great, the mother of the fornications, and the abominations of the earth.
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
And I saw the woman drunk with the blood of the saints, and with the blood of the martyrs of Jesus. And I wondered, when I had seen her, with great admiration.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And the angel said to me: Why dost thou wonder? I will tell thee the mystery of the woman, and of the beast which carrieth her, which hath the seven heads and ten horns.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos )
The beast, which thou sawest, was, and is not, and shall come up out of the bottomless pit, and go into destruction: and the inhabitants on the earth (whose names are not written in the book of life from the foundation of the world) shall wonder, seeing the beast that was, and is not. (Abyssos )
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
And here is the understanding that hath wisdom. The seven heads are seven mountains, upon which the woman sitteth, and they are seven kings:
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
Five are fallen, one is, and the other is not yet come: and when he is come, he must remain a short time.
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
And the beast which was, and is not: the same also is the eighth, and is of the seven, and goeth into destruction.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
And the ten horns which thou sawest, are ten kings, who have not yet received a kingdom, but shall receive power as kings one hour after the beast.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
These have one design: and their strength and power they shall deliver to the beast.
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
These shall fight with the Lamb, and the Lamb shall overcome them, because he is Lord of lords, and King of kings, and they that are with him are called, and elect, and faithful.
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
And he said to me: The waters which thou sawest, where the harlot sitteth, are peoples, and nations, and tongues.
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
And the ten horns which thou sawest in the beast: these shall hate the harlot, and shall make her desolate and naked, and shall eat her flesh, and shall burn her with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
For God hath given into their hearts to do that which pleaseth him: that they give their kingdom to the beast, till the words of God be fulfilled.
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
And the woman which thou sawest, is the great city, which hath kingdom over the kings of the earth.