< Ru’uya ta Yohanna 17 >
1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
And one of the seven agents who had the seven bowls came and spoke with me, saying, Come, I will show thee the judgment of the great whore who sits upon the many waters
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
with whom the kings of the earth fornicated, and those who inhabit the earth were made drunken with the wine of her fornication.
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And he carried me away in spirit into a wilderness. And I saw a woman sitting upon a scarlet-colored beast containing names of blasphemy, having seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
And the woman was clothed in purple and scarlet, adorned with gold and precious stone and pearls, having in her hand a golden cup containing abominations and the filthy things of her fornication,
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
and upon her forehead a name written, MYSTERY, BABYLON THE GREAT, THE MOTHER OF WHORES AND OF THE ABOMINATIONS OF THE EARTH.
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
And I saw the woman drunken from the blood of the sanctified, and from the blood of the witnesses of Jesus. And having seen her, I wondered with great amazement.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And the agent said to me, Why did thou wonder? I will tell thee the mystery of the woman, and of the beast that carries her, which has the seven heads and the ten horns.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos )
The beast that thou saw was, and is not, and is going to ascend out of the abyss and go into destruction. And those who dwell on the earth will wonder, whose names have not been written in the book of life from the foundation of the world, when they see the beast that was, and is not, and will come. (Abyssos )
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
Here is the mind that has wisdom: The seven heads are seven mountains where the woman sits on them.
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
And there are seven kings, the five are fallen, the one is, the other has not yet come, and when he comes he must remain a little while.
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
And the beast that was, and is not, he also is an eighth, and is of the seven, and he goes into destruction.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
And the ten horns that thou saw are ten kings who have not yet received a kingdom, but they receive authority as kings one hour with the beast.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
These have one mind, and they give their power and authority to the beast.
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
These will war against the Lamb, and the Lamb will conquer them, because he is Lord of lords and King of kings. And those with him are the called and chosen and faithful.
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
And he says to me, The waters that thou saw, where the whore sits, are peoples, and multitudes, and nations, and tongues.
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
And the ten horns that thou saw, and the beast, these will hate the whore, and will make her desolate, and will make her naked, and will eat her flesh, and will burn her with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
For God gave in their hearts to do his will. Even to do one will, and to give their kingdom to the beast until the words of God would be ended.
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
And the woman whom thou saw is the great city having reign over the kings of the earth.