< Ru’uya ta Yohanna 16 >

1 Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
In slišal sem glas velik iz svetišča govoreč sedmerim angelom: "Pojdite in izlijte čaše jeze Božje na zemljo.
2 Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
In otide prvi ter izlije čašo svojo na zemljo; in naredi se ulé hudo in strupeno na ljudî imajoče znamenje zveri, in nje, ki so molili njeno podobo.
3 Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
In drugi angelj izlije čašo svojo v morje; in naredi se kri kakor mrliča; in vsaka duša živa umrje v morji.
4 Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
In tretji angelj izlije čašo svojo v reke in studence vodâ; in naredi se kri.
5 Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
In slišal sem angela vodâ govorečega: Pravičen si, Gospod, kateri si in si bil in sveti, ker si to sodil;
6 gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
Ker kri svetnikov in prerokov so prelili, in krvi si jim dal piti; kajti vredni so.
7 Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
In slišal sem druzega od oltarja govorečega: Dà, Gospod, Bog vsemogočni, resnične in pravične so sodbe tvoje.
8 Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
In četrti angelj izlije čašo svojo na solnce; in dalo se mu je ljudî izžgati v ognji;
9 Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
In izžgali so se ljudje v silni vročini, in preklinjali so ime Boga, ki ima oblast do teh šib, in niso se izpokorili, da bi mu slavo dajali.
10 Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
In peti angelj izlije čašo svojo na prestol zveri; in kraljestvo njeno je otemnélo; in grizli so si jezike svoje od muke,
11 suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
In preklinjali so Boga nebeškega od muk svojih in od ulés svojih, in niso se izpokorili od svojih del.
12 Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
In šesti angelj izlije čašo svojo na reko véliko Evfrat; in posuši se voda njena, da se pripravi pot kraljev od solnčnega vzhoda.
13 Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
In videl sem iz ust zmajevih in iz ust zveri in iz ust lažipreroka tri nečiste duhove enake žabam;
14 Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
So namreč duhovi hudičev, ki delajo znamenja, kateri izhajajo na kralje zemlje in vesoljnega sveta, da jih zberó na vojsko tistega velikega dné Boga vsemogočnega.
15 “Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
Glej, pridem kakor tat, in blagor mu, kdor čuje in hrani oblačila svoja, da ne hodi nag in ne gledajo sramote njegove.
16 Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
In zbere jih na kraj imenovan po hebrejsko: Harmagedon.
17 Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
In sedmi angelj izlije čašo svojo v zrak; in izšel je glas velik od svetišča nebeškega, izpred prestola, govoreč: Zgodilo se je!
18 Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
In nastanejo glasovi in gromi in bliski, in potres nastane velik, kakoršnega ni bilo, odkar so ljudje bili na zemlji; tolik potres, tako velik!
19 Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
In mesto véliko postane na tri dele, in mesta narodov padejo; in Babilona vélikega so se spomnili pred Bogom, dati mu čašo vina omotnega jeze njegove.
20 Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
In vsi otoki so bežali, in gorâ ni bilo najti.
21 Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.
In toča velika, skoraj talent težka pada dol iz neba na ljudî; in preklinjali so ljudje Boga zaradi šibe toče, ker velika je šiba njena silno.

< Ru’uya ta Yohanna 16 >