< Ru’uya ta Yohanna 16 >

1 Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
Then I heard a loud voice from the sanctuary say to the seven angels, "Go and pour on to the earth the seven bowls of the anger of God."
2 Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
So the first angel went away and poured his bowl on to the earth; and it brought a bad and painful sore upon the men who had on them the mark of the Wild Beast and worshipped his statue.
3 Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
The second angel poured his bowl into the sea, and it became blood, like a dead man's blood, and every living creature in the sea died.
4 Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
The third angel poured his bowl into the rivers and springs of water, and they became blood.
5 Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
And I heard the angel of the waters say, "Righteous art Thou, who art and wast, the holy One, because Thou hast thus taken vengeance.
6 gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
For they poured out the blood of Thy people and of the Prophets, and in return Thou hast given them blood to drink. And this they deserved."
7 Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
And I heard a voice from the altar say, "Even so, O Lord God, the Ruler of all, true and righteous are Thy judgments."
8 Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
Then the fourth angel poured his bowl on to the sun, and power was given to it to scorch men with fire.
9 Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
And the men were severely burned; and yet they spoke evil of God who had power over the plagues, and they did not repent so as to give Him glory.
10 Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
The fifth angel poured his bowl on to the throne of the Wild Beast; and his kingdom became darkened. People gnawed their tongues because of the pain,
11 suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
and they spoke evil of the God in Heaven because of their pains and their sores, and did not repent of their misconduct.
12 Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
The sixth angel poured his bowl into that great river, the Euphrates; and its stream was dried up in order to clear the way for the kings who are to come from the east.
13 Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
Then I saw three foul spirits, resembling frogs, issue from the mouth of the Dragon, from the mouth of the Wild Beast, and from the mouth of the false Prophet.
14 Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
For they are the spirits of demons working marvels--spirits that go out to control the kings of the whole earth, to assemble them for the battle which is to take place on the great day of God, the Ruler of all.
15 “Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
("I am coming like a thief. Blessed is the man who keeps awake and guards his raiment for fear he walk about ill-clad, and his uncomeliness become manifest.")
16 Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
And assemble them they did at the place called in Hebrew 'Har-Magedon.'
17 Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
Then the seventh angel poured his bowl into the air; and a loud voice came out of the sanctuary from the throne, saying, "Everything is now ready."
18 Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
Flashes of lightning followed, and voices, and peals of thunder, and an earthquake more dreadful than there had ever been since there was a man upon the earth--so terrible was it, and so great!
19 Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
The great city was split into three parts; the cities of the nations fell; and great Babylon came into remembrance before God, for Him to make her drink from the wine-cup of His fierce anger.
20 Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
Every island fled away, and there was not a mountain anywhere to be seen.
21 Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.
And heavy hail, that seemed to be a talent in weight, fell from the sky upon the people; and they spoke evil of God on account of the plague of the hail--because the plague of it was exceedingly severe.

< Ru’uya ta Yohanna 16 >