< Ru’uya ta Yohanna 15 >

1 Na ga wata babbar alama mai banmamaki a sama, mala’iku bakwai da annobai bakwai na ƙarshe, na ƙarshe, domin da su ne fushin Allah ya cika.
Then I saw another marvel in Heaven, great and wonderful--there were seven angels bringing seven plagues. These are the last plagues, because in them God's anger has found full expression.
2 Sai na ga abin da ya yi kamar tekun gilashi gauraye da wuta kuma tsaye kusa da teku, waɗanda suka ci nasara bisan dabbar da siffarta da bisan lambar sunanta. Suna riƙe da garayu waɗanda Allah ya ba su
And I saw what seemed to be a sea of glass mingled with fire, and those who had gained the victory over the Wild Beast and over his statue and the number of his name, standing by the sea of glass and having harps which belonged to God.
3 suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
And they were singing the song of Moses, God's servant, and the song of the Lamb. Their words were, "Great and wonderful are Thy works, O Lord God, the Ruler of all. Righteous and true are Thy ways, O King of the nations.
4 Wane ne ba zai ji tsoronka, yă kuma kawo ɗaukaka ga sunanka ba, ya Ubangiji? Gama kai kaɗai ne mai tsarki. Dukan al’ummai za su zo su yi sujada a gabanka, gama an bayyana ayyukan adalcinka.”
Who shall not be afraid, O Lord, and glorify Thy name? For Thou alone art holy. All nations shall come and shall worship Thee, because the righteousness of all that Thou hast done has been made manifest."
5 Bayan wannan sai na duba, a cikin sama kuwa sai ga haikali, wato, tabanakul na Shaida, a buɗe.
After this, when the doors of the sanctuary of the tent of witness in Heaven were opened, I looked;
6 Daga cikin haikalin mala’iku bakwai tare da annobai bakwai suka fito. Suna saye da tufafin lilin masu tsabta masu walƙiya, suna kuma saye da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.
and there came out of the sanctuary the seven angels who were bringing the seven plagues. The angels were clad in pure, bright linen, and had girdles of gold across their breasts.
7 Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn g165)
And one of the four living creatures gave the seven angels seven bowls of gold, full of the anger of God who lives until the Ages of the Ages. (aiōn g165)
8 Aka kuma cika haikalin da hayaƙi daga ɗaukakar Allah da kuma daga ikonsa, kuma ba wanda ya iya shiga haikalin sai da aka cika annobai bakwai nan na mala’iku bakwai.
And the sanctuary was filled with smoke from the glory of God and from His power; and no one could enter the sanctuary till the seven plagues brought by the seven angels were at an end.

< Ru’uya ta Yohanna 15 >