< Ru’uya ta Yohanna 15 >
1 Na ga wata babbar alama mai banmamaki a sama, mala’iku bakwai da annobai bakwai na ƙarshe, na ƙarshe, domin da su ne fushin Allah ya cika.
And I saw another prodigy in heaven, great and wonderful; seven angels, having seven plagues, the last in order, because with them the wrath of God is consummated.
2 Sai na ga abin da ya yi kamar tekun gilashi gauraye da wuta kuma tsaye kusa da teku, waɗanda suka ci nasara bisan dabbar da siffarta da bisan lambar sunanta. Suna riƙe da garayu waɗanda Allah ya ba su
And I saw as it were, a sea of glass mixed with fire: and they, who had been victorious over the beast of prey, and over its image, and over the number of its name, were standing on the sea of glass; and they had the harps of God.
3 suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
And they sing the song of Moses the servant of God, and the song of the Lamb, saying: Great and marvellous are thy deeds, Lord God Almighty; just and true are thy ways, O King of worlds.
4 Wane ne ba zai ji tsoronka, yă kuma kawo ɗaukaka ga sunanka ba, ya Ubangiji? Gama kai kaɗai ne mai tsarki. Dukan al’ummai za su zo su yi sujada a gabanka, gama an bayyana ayyukan adalcinka.”
Who shall not fear thee, O Lord, and glorify thy name? Because thou only art holy and just: Because all nations shall come and worship before thee, since thy righteousnesses have been revealed.
5 Bayan wannan sai na duba, a cikin sama kuwa sai ga haikali, wato, tabanakul na Shaida, a buɗe.
And after this I beheld, and the temple of the tabernacle of the testimony in heaven, was opened.
6 Daga cikin haikalin mala’iku bakwai tare da annobai bakwai suka fito. Suna saye da tufafin lilin masu tsabta masu walƙiya, suna kuma saye da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.
And the seven angels who had the seven plagues, went forth from the temple, clothed in clean splendid linen, and girded about their breast with girdles of gold.
7 Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn )
And one of the four Animals gave to those seven angels seven cups of gold, full of the wrath of God who liveth for ever and ever. (aiōn )
8 Aka kuma cika haikalin da hayaƙi daga ɗaukakar Allah da kuma daga ikonsa, kuma ba wanda ya iya shiga haikalin sai da aka cika annobai bakwai nan na mala’iku bakwai.
And the temple was filled with smoke, from the glory of God and from his power; and no one was able to enter the temple, until the seven plagues of the seven angels were accomplished.