< Ru’uya ta Yohanna 15 >
1 Na ga wata babbar alama mai banmamaki a sama, mala’iku bakwai da annobai bakwai na ƙarshe, na ƙarshe, domin da su ne fushin Allah ya cika.
And I saw another sign in heaven, great and marvellous, —seven messengers having seven plagues, the last, because, in them, was ended the wrath of God.
2 Sai na ga abin da ya yi kamar tekun gilashi gauraye da wuta kuma tsaye kusa da teku, waɗanda suka ci nasara bisan dabbar da siffarta da bisan lambar sunanta. Suna riƙe da garayu waɗanda Allah ya ba su
And I saw as a glassy sea mingled with fire, and them who escape victorious from the beast, and from his image, and from the number of his name, standing upon the glassy sea, having harps of God;
3 suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
and they sing the song of Moses the servant of God and the song of the Lamb, saying—Great and marvelous, are thy works, Lord, God, the Almighty! Righteous and true, are thy ways, O King of the ages!
4 Wane ne ba zai ji tsoronka, yă kuma kawo ɗaukaka ga sunanka ba, ya Ubangiji? Gama kai kaɗai ne mai tsarki. Dukan al’ummai za su zo su yi sujada a gabanka, gama an bayyana ayyukan adalcinka.”
Who shall in anywise not be put in fear, O Lord, and glorify thy name, —because, alone, full of lovingkindness; because, all the nations, will have come, and will do homage before thee, because, thy righteous deeds, were made manifest?
5 Bayan wannan sai na duba, a cikin sama kuwa sai ga haikali, wato, tabanakul na Shaida, a buɗe.
And, after these things, I saw, and the sanctuary of The Tent of Witness in heaven, was opened;
6 Daga cikin haikalin mala’iku bakwai tare da annobai bakwai suka fito. Suna saye da tufafin lilin masu tsabta masu walƙiya, suna kuma saye da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.
And the seven messengers who had the seven plagues, came forth, out of the sanctuary clothed with a [precious] stone, pure, bright, and girt about the breasts with girdles of gold.
7 Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn )
And, one of the four living creatures, gave, unto the seven messengers, seven golden bowls, full of the wrath of God who liveth unto the ages of ages. (aiōn )
8 Aka kuma cika haikalin da hayaƙi daga ɗaukakar Allah da kuma daga ikonsa, kuma ba wanda ya iya shiga haikalin sai da aka cika annobai bakwai nan na mala’iku bakwai.
And the sanctuary was filled with smoke by reason of the glory of God, and by reason of his power; and, no one, was able to enter into the sanctuary, until the seven plagues of the seven messengers should be ended.