< Ru’uya ta Yohanna 14 >
1 Sai na duba, can a gabana kuwa ga Ɗan Rago, tsaye a kan Dutsen Sihiyona, tare da shi akwai kuma mutane 144,000 waɗanda suke da sunansa da sunan Ubansa a rubuce a goshinsu.
Then I looked, and behold, the Lamb was standing on Mount Zion, and with him was a multitude numbering one hundred forty-four thousand, who had his name and the name of his Father written on their foreheads.
2 Sai na ji ƙara daga sama kamar motsin ruwaye masu gudu, kamar kuma tsawa. Ƙarar da na ji ta yi kamar ta masu garaya da suke kiɗin garayarsu.
And I heard a voice from heaven like the roar of many waters and like the sound of great thunder. The voice I heard was like the sound of harpists playing their harps.
3 Suka kuwa rera sabuwar waƙa a gaban kursiyin da kuma a gaban halittu huɗun nan masu rai, da kuma a gaban dattawa. Ba wanda ya iya koyon waƙar sai mutanen nan 144,000 da aka fansa daga duniya.
They were singing a new song before the throne and before the four living creatures and the elders. No one could learn the song except the one hundred forty-four thousand who had been redeemed from the earth.
4 Waɗannan su ne waɗanda ba su ƙazantar da kansu da mata ba, gama sun kiyaye kansu da tsarki. Suna bin Ɗan Ragon duk inda ya tafi. Su ne aka saya daga cikin mutane aka kuwa miƙa su kamar’ya’yan fari ga Allah da kuma Ɗan Ragon.
These are the ones who have not defiled themselves with women, for they are virgins. These are the ones who follow the Lamb wherever he goes. They have been redeemed by Jesus from among men as firstfruits to God and the Lamb.
5 Ba a sami ƙarya a bakunansu ba; su kuma marasa aibi ne.
No lie was found in their mouths, for they are blameless.
6 Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios )
Then I saw an angel flying directly overhead, with an eternal gospel to preach to those who dwell on the earth, to every nation, tribe, tongue, and people. (aiōnios )
7 Ya ce da babbar murya, “Ku ji tsoron Allah ku kuma ɗaukaka shi, domin sa’ar hukuncinsa ya yi. Ku yi wa wannan da ya halicci sammai, ƙasa, teku, da maɓulɓulan ruwa sujada.”
He said with a loud voice, “Fear the Lord and give him glory, because the hour of his judgment has come. Worship him who made heaven and earth, the sea and the springs of water.”
8 Mala’ika na biyu ya biyo yana cewa, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi, wadda ta sa dukan al’ummai suka sha ruwan inabin hauka na zinanta.”
A second angel followed, saying, “Fallen is Babylon the great! She has made all the nations drink of the wine of the wrath of her fornication.”
9 Mala’ika na uku ya biyo su ya ce da babbar murya, “Duk wanda ya yi wa dabban nan da siffarta sujada ya kuma sami alamarta a goshi ko a hannu,
A third angel followed them, saying with a loud voice, “If anyone worships the beast and his image, and receives a mark on his forehead or his hand,
10 shi ma zai sha ruwan inabin fushin Allah, wanda aka zuba da duk ƙarfinsa a kwaf fushinsa. Za a ba shi azaba da farar wuta mai ci a gaban tsarkakan mala’iku da na Ɗan Ragon.
he too will drink of the wine of the wrath of God that has been mixed undiluted in the cup of his anger. He will be tormented with fire and sulfur in the presence of the holy angels and in the presence of the Lamb.
11 Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn )
And the smoke of their torment goes up forever and ever. There is no rest day or night for those who worship the beast and his image or for anyone who receives the mark of his name.” (aiōn )
12 Wannan yana bukata haƙuri, a gefen tsarkakan da suke biyayya da umarnan Allah suka kuma kasance da aminci ga Yesu.
This calls for the endurance of the saints, those who keep the commandments of God and hold fast to their faith in Jesus.
13 Sai na ji murya daga sama ta ce, “Rubuta, Masu albarka ne matattun da suka mutu cikin Ubangiji daga yanzu zuwa gaba.” “I, za su huta daga faman aikinsu, gama ayyukansu za su bi su,” in ji Ruhu.
Then I heard a voice from heaven saying, “Write: ‘Blessed are the dead who die in the Lord from now on.’” “Yes,” says the Spirit, “that they may rest from their labors, and their works will follow them.”
14 Na duba, can gabana kuwa ga farin girgije, zaune kuma a kan girgijen kuwa ga wani da ya yi kamar “ɗan mutum” tare da rawanin zinariya a kansa da kuma lauje mai kaifi a hannunsa.
Then I looked, and behold, there was a white cloud, and sitting on the cloud was one like a son of man, with a golden crown on his head and a sharp sickle in his hand.
15 Sai wani mala’ika ya fito daga haikali ya kuma yi kira da babbar murya ga wannan mai zaune a kan girgijen ya ce, “Ɗauki laujenka ka yi girbi, domin lokacin girbi ya yi, gama amfanin da yake duniya ya nuna.”
And another angel came out of the temple, crying out with a loud voice to him who was sitting on the cloud, “Take yoʋr sickle and reap, because the hour to reap has come, for the harvest of the earth is ripe.”
16 Sai wannan mai zaune a girgijen ya wurga laujensa a duniya, sai aka kuwa girbe duniya.
So he who was sitting on the cloud swung his sickle over the earth, and the earth was reaped.
17 Wani mala’ika kuma ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da lauje mai kaifi.
Then another angel came out of the temple in heaven; he too had a sharp sickle.
18 Har yanzu, wani mala’ika mai lura da wuta, ya fito daga bagaden ya yi kira da babbar murya ga wannan wanda yake da lauje mai kaifi ya ce, “Ɗauki laujenka mai kaifi ka tattara kawunan’ya’yan inabi daga kuringar inabin duniya, domin’ya’yan inabin sun nuna.”
And another angel, who had authority over the fire, came out from the altar and called out with a loud cry to the angel who had the sharp sickle, “Take yoʋr sharp sickle and gather the clusters from the vintage of the earth, for the grapes of the earth are ripe.”
19 Mala’ikan ya wurga laujensa a duniya, ya tattara’ya’yan inabin, ya kuma zuba su cikin babbar wurin matsewar inabin fushin Allah.
So the angel swung his sickle across the earth, gathered the vintage of the earth, and threw it into the great winepress of the wrath of God.
20 Aka tattake su a wurin matsin inabi a bayan gari, jini kuwa ya yi ta gudana daga wurin matsin inabi tsayinsa ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, nisansa kuma ya kai wajen kilomita 300.
Then the winepress was trodden outside the city, and blood came out of the winepress, as high as a horse's bridle, for one thousand six hundred stadia.