< Ru’uya ta Yohanna 14 >
1 Sai na duba, can a gabana kuwa ga Ɗan Rago, tsaye a kan Dutsen Sihiyona, tare da shi akwai kuma mutane 144,000 waɗanda suke da sunansa da sunan Ubansa a rubuce a goshinsu.
AND I saw, and lo, a lamb stood upon the mount Zion, and with him an hundred forty-four thousand, having the name of his Father inscribed on their foreheads.
2 Sai na ji ƙara daga sama kamar motsin ruwaye masu gudu, kamar kuma tsawa. Ƙarar da na ji ta yi kamar ta masu garaya da suke kiɗin garayarsu.
And I heard a voice from heaven, as the sound of many waters, and as the roar of loud thunder; and I heard the sound of harpers harping on their harps:
3 Suka kuwa rera sabuwar waƙa a gaban kursiyin da kuma a gaban halittu huɗun nan masu rai, da kuma a gaban dattawa. Ba wanda ya iya koyon waƙar sai mutanen nan 144,000 da aka fansa daga duniya.
and they sang as it were a new song before the throne, and before the four living beings, and the presbyters: and no person could learn that song, but the hundred forty-four thousand, who were redeemed from the earth.
4 Waɗannan su ne waɗanda ba su ƙazantar da kansu da mata ba, gama sun kiyaye kansu da tsarki. Suna bin Ɗan Ragon duk inda ya tafi. Su ne aka saya daga cikin mutane aka kuwa miƙa su kamar’ya’yan fari ga Allah da kuma Ɗan Ragon.
These are they who have not defiled themselves with women; for they are virgins: these are they who follow the Lamb whithersoever he goeth: these have been redeemed among men, as first-fruits to God, and to the Lamb.
5 Ba a sami ƙarya a bakunansu ba; su kuma marasa aibi ne.
And in their mouth no guile is found; for they are blameless before the throne of God.
6 Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios )
And I saw another angel flying in the midst of heaven, having the everlasting gospel to preach the glad tidings to the inhabitants of the earth, to every nation, and tribe, and tongue, and people, (aiōnios )
7 Ya ce da babbar murya, “Ku ji tsoron Allah ku kuma ɗaukaka shi, domin sa’ar hukuncinsa ya yi. Ku yi wa wannan da ya halicci sammai, ƙasa, teku, da maɓulɓulan ruwa sujada.”
saying with a loud voice, Fear God, and give him glory; for the hour of his judgment is come; and worship him that made the heaven and the earth, and the sea, and the fountains of waters.
8 Mala’ika na biyu ya biyo yana cewa, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi, wadda ta sa dukan al’ummai suka sha ruwan inabin hauka na zinanta.”
And another angel followed, saying, Babylon is fallen, is fallen, that great city, because all nations have been made to drink of the wine of the wrath of her whoredom.
9 Mala’ika na uku ya biyo su ya ce da babbar murya, “Duk wanda ya yi wa dabban nan da siffarta sujada ya kuma sami alamarta a goshi ko a hannu,
And a third angel followed them, saying with a loud voice, If any person worship the beast, and his image, and receive the brand upon his forehead, and upon his right hand,
10 shi ma zai sha ruwan inabin fushin Allah, wanda aka zuba da duk ƙarfinsa a kwaf fushinsa. Za a ba shi azaba da farar wuta mai ci a gaban tsarkakan mala’iku da na Ɗan Ragon.
he also shall drink of the wine of the fury of God, which is mixed undiluted with water in the cup of his wrath; and he shall be tormented with fire and brimstone in the presence of the holy angels, and in the presence of the Lamb:
11 Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn )
and the smoke of their torment ascendeth for ever and ever: and they have no respite day nor night, who worship the beast and his image, and whosoever receiveth the brand of his name. (aiōn )
12 Wannan yana bukata haƙuri, a gefen tsarkakan da suke biyayya da umarnan Allah suka kuma kasance da aminci ga Yesu.
Here is the patience of the saints: here are they who keep the commandments of God, and the faith of Jesus.
13 Sai na ji murya daga sama ta ce, “Rubuta, Masu albarka ne matattun da suka mutu cikin Ubangiji daga yanzu zuwa gaba.” “I, za su huta daga faman aikinsu, gama ayyukansu za su bi su,” in ji Ruhu.
And I heard a voice from heaven saying to me, Write, Blessed are the dead who die in the Lord, from henceforward: yea, saith the Spirit, that they may have rest from their labours; but their works follow after them.
14 Na duba, can gabana kuwa ga farin girgije, zaune kuma a kan girgijen kuwa ga wani da ya yi kamar “ɗan mutum” tare da rawanin zinariya a kansa da kuma lauje mai kaifi a hannunsa.
And I saw, and, lo! a white cloud, and upon the cloud sat one like to a son of man, having on his head a golden crown, and in his hand a sharp sickle.
15 Sai wani mala’ika ya fito daga haikali ya kuma yi kira da babbar murya ga wannan mai zaune a kan girgijen ya ce, “Ɗauki laujenka ka yi girbi, domin lokacin girbi ya yi, gama amfanin da yake duniya ya nuna.”
And anther angel came forth out of the temple, crying with a loud voice to him that sat upon the cloud, Put in thy sickle, and reap: for the hour is come for thee to reap; because the harvest of the earth is fully ripe.
16 Sai wannan mai zaune a girgijen ya wurga laujensa a duniya, sai aka kuwa girbe duniya.
And he who sat on the cloud thrust in his sickle upon the earth, and the earth was reaped.
17 Wani mala’ika kuma ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da lauje mai kaifi.
And another angel came forth out of the temple which is in heaven, having also himself a sharp sickle.
18 Har yanzu, wani mala’ika mai lura da wuta, ya fito daga bagaden ya yi kira da babbar murya ga wannan wanda yake da lauje mai kaifi ya ce, “Ɗauki laujenka mai kaifi ka tattara kawunan’ya’yan inabi daga kuringar inabin duniya, domin’ya’yan inabin sun nuna.”
And another angel came forth from the altar, having authority over fire; and he cried with a loud voice to him who held the sharp sickle, saying, Put in thy sharp sickle, and gather the bunches of the vine of the earth; for her clusters are ripe.
19 Mala’ikan ya wurga laujensa a duniya, ya tattara’ya’yan inabin, ya kuma zuba su cikin babbar wurin matsewar inabin fushin Allah.
And the angel thrust in his sickle upon the earth, and gathered the grapes of the vine of the earth, and cast them into the great winepress of the wrath of God.
20 Aka tattake su a wurin matsin inabi a bayan gari, jini kuwa ya yi ta gudana daga wurin matsin inabi tsayinsa ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, nisansa kuma ya kai wajen kilomita 300.
And the wine-press was trodden without the city, and blood issued from the wine-press, as high as the horses’ bridles, for the space of a thousand and six hundred furlongs.