< Ru’uya ta Yohanna 14 >
1 Sai na duba, can a gabana kuwa ga Ɗan Rago, tsaye a kan Dutsen Sihiyona, tare da shi akwai kuma mutane 144,000 waɗanda suke da sunansa da sunan Ubansa a rubuce a goshinsu.
And I saw, and behold, the Lamb standing on the mount Zion, and with him a hundred and forty-four thousand, having his name, and the name of his Father written on their foreheads.
2 Sai na ji ƙara daga sama kamar motsin ruwaye masu gudu, kamar kuma tsawa. Ƙarar da na ji ta yi kamar ta masu garaya da suke kiɗin garayarsu.
And I heard a voice from heaven, as the sound of many waters, and as the sound of a great thunder: and the sound which I heard was as the sound of harpers harping with their harps:
3 Suka kuwa rera sabuwar waƙa a gaban kursiyin da kuma a gaban halittu huɗun nan masu rai, da kuma a gaban dattawa. Ba wanda ya iya koyon waƙar sai mutanen nan 144,000 da aka fansa daga duniya.
and they are singing a new song before the throne, and in presence of the four living creatures, and the elders. And no one was able to learn the song except the hundred and forty-four thousand, who have been redeemed from the earth.
4 Waɗannan su ne waɗanda ba su ƙazantar da kansu da mata ba, gama sun kiyaye kansu da tsarki. Suna bin Ɗan Ragon duk inda ya tafi. Su ne aka saya daga cikin mutane aka kuwa miƙa su kamar’ya’yan fari ga Allah da kuma Ɗan Ragon.
These are they who have not been defiled with women; for they are virgins. These are they who follow the Lamb whithersoever he may go. They have been redeemed from men, the first fruit unto God and the Lamb.
5 Ba a sami ƙarya a bakunansu ba; su kuma marasa aibi ne.
And in their mouth no lie is found: for they are blameless.
6 Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios )
And I saw another angel flying in the midst of heaven having the eternal gospel to preach to those dwelling upon the earth, and to every nation, and tribe, and tongue, and people, (aiōnios )
7 Ya ce da babbar murya, “Ku ji tsoron Allah ku kuma ɗaukaka shi, domin sa’ar hukuncinsa ya yi. Ku yi wa wannan da ya halicci sammai, ƙasa, teku, da maɓulɓulan ruwa sujada.”
saying with a great voice, Fear God, and give glory to him; because the hour of his judgment is come: and worship him who made the heaven, and the earth, and the sea, and the fountains of the waters.
8 Mala’ika na biyu ya biyo yana cewa, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi, wadda ta sa dukan al’ummai suka sha ruwan inabin hauka na zinanta.”
And another second angel followed, saying, Fallen, fallen is Babylon the great, who has made all the nation to drink of the wine of the wrath of her fornication.
9 Mala’ika na uku ya biyo su ya ce da babbar murya, “Duk wanda ya yi wa dabban nan da siffarta sujada ya kuma sami alamarta a goshi ko a hannu,
And another, the third angel followed these, saying with a great voice, If any one worships the beast and his image, and receives a mark upon his forehead, or upon his hand,
10 shi ma zai sha ruwan inabin fushin Allah, wanda aka zuba da duk ƙarfinsa a kwaf fushinsa. Za a ba shi azaba da farar wuta mai ci a gaban tsarkakan mala’iku da na Ɗan Ragon.
and he shall drink of the wine of the wrath of God, having been poured out without mixture in the cup of his indignation; and he shall be tormented with fire and brimstone in the presence of the holy angels, and in the presence of the Lamb.
11 Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn )
And the smoke of their torment, ascends up into ages of ages: and they have no rest day and night, who worship the beast and his image, and if any one receives the mark of his name. (aiōn )
12 Wannan yana bukata haƙuri, a gefen tsarkakan da suke biyayya da umarnan Allah suka kuma kasance da aminci ga Yesu.
Here is the faith of the saints: who keep the commandments of God and the faith of Jesus.
13 Sai na ji murya daga sama ta ce, “Rubuta, Masu albarka ne matattun da suka mutu cikin Ubangiji daga yanzu zuwa gaba.” “I, za su huta daga faman aikinsu, gama ayyukansu za su bi su,” in ji Ruhu.
And I heard a voice from the heaven saying, Write; Blessed are the dead immediately, who die in the Lord. Yea, says the Spirit, that they shall rest from their labors; for their works do follow along with them.
14 Na duba, can gabana kuwa ga farin girgije, zaune kuma a kan girgijen kuwa ga wani da ya yi kamar “ɗan mutum” tare da rawanin zinariya a kansa da kuma lauje mai kaifi a hannunsa.
And I saw, and behold a white cloud, and on the cloud one sitting like the Son of man, having on his head a golden crown, and in his hand a sharp sickle.
15 Sai wani mala’ika ya fito daga haikali ya kuma yi kira da babbar murya ga wannan mai zaune a kan girgijen ya ce, “Ɗauki laujenka ka yi girbi, domin lokacin girbi ya yi, gama amfanin da yake duniya ya nuna.”
And another angel came out of the temple, crying with a great voice to the one sitting on the cloud, Send forth your sickle, and reap: because the hour of reaping has come; because the harvest of the earth is fully ripe.
16 Sai wannan mai zaune a girgijen ya wurga laujensa a duniya, sai aka kuwa girbe duniya.
And the one sitting on the cloud thrust in his sickle to the earth; and the earth was reaped.
17 Wani mala’ika kuma ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da lauje mai kaifi.
And another angel came out of the temple which is in heaven, himself also having a sharp sickle:
18 Har yanzu, wani mala’ika mai lura da wuta, ya fito daga bagaden ya yi kira da babbar murya ga wannan wanda yake da lauje mai kaifi ya ce, “Ɗauki laujenka mai kaifi ka tattara kawunan’ya’yan inabi daga kuringar inabin duniya, domin’ya’yan inabin sun nuna.”
and another angel came out from the altar, having power over the fire; and he called with a great voice to the one having the sharp sickle, Send in thy sharp sickle, and reap the clusters of the vintage of the earth; because her grapes are fully ripe.
19 Mala’ikan ya wurga laujensa a duniya, ya tattara’ya’yan inabin, ya kuma zuba su cikin babbar wurin matsewar inabin fushin Allah.
And the angel cast his sickle into the earth, and reaped the vintage of the earth, and cast it into the great wine-press of the wrath of God.
20 Aka tattake su a wurin matsin inabi a bayan gari, jini kuwa ya yi ta gudana daga wurin matsin inabi tsayinsa ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, nisansa kuma ya kai wajen kilomita 300.
And the winepress was trodden without the city, and blood came out from the winepress, unto the trappings of the horses, one thousand and six hundred furlongs.